fidelitybank

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Date:

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a jam’iyyar PDP, dan takarar gwamna, Adamu Maina Waziri, ya koma African Democratic Congress, (ADC), a jihar Yobe.

Hakan ya biyo bayan ficewar sa daga jam’iyyar PDP a ranar Litinin a karamar hukumar Potiskum ta jihar.

Ya mika takardar murabus dinsa ga Shugaban Unguwa a Unguwar Dogo-tebo da ke Potiskum.

Waziri, mamban kwamitin amintattu na PDP, ya yi nuni da cewa “jagoranci da alkiblar PDP a halin yanzu bai dace da babbar jam’iyyar siyasa ba,” ya kara da cewa jam’iyyar “ta rasa matsayinta na ‘yan adawa na farko.”

Ya yi alkawarin tattara abokansa na siyasa don shiga ADC, yana mai kira ga wasu da su shiga cikin wani yunkuri na maido da fata na dimokradiyya a kasar.

Ficewar Waziri ya zo daidai da taron jam’iyyar ADC na shiyyar Potiskum a garin Potiskum, inda shugabannin jam’iyyar suka yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga matasa da mata da tsofaffi da su shiga jam’iyyar ADC domin ciyar da kasa gaba.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a...

Trump ya caccaki Elon Musk

Shugaban Amurka Donald Trump ya caccaki tsohon mashawarcinsa, Elon...

Dalilin da ya sa Kwankwaso ya ki shiga jam’iyyar hadaka – Galadima

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...

Obi ba zai taba zama shugaban kasa ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce, tsohon ɗan takarar...

Ƴansanda sun kama ƴan Ghana 19 da aka yi safararsu a Najeriya

Rundunar ƴansandan Najeriya ta kuɓutar da wasu ƴan Ghana...

Benue da Edo da Bayelsa na fargabar balewar madatsar ruwan Kamaru

Gwamnatocin jihohi uku na cikin shirin ko-ta -kwana, sakamakon...

Jihohin Najeriya tara da za a iya samun ambaliya ciki harda Kano

Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya Nimet, ta yi hasashen...

Tsohon sakataren gwamnatin a mulkin Buhari ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, SGF, Babachir Lawal ya fice...

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...
X whatsapp