fidelitybank

Tsohon Ministan kuma jigo a PDP ya koma ADC

Date:

Tsohon ministan harkokin ‘yan sanda kuma sau uku a jam’iyyar PDP, dan takarar gwamna, Adamu Maina Waziri, ya koma African Democratic Congress, (ADC), a jihar Yobe.

Hakan ya biyo bayan ficewar sa daga jam’iyyar PDP a ranar Litinin a karamar hukumar Potiskum ta jihar.

Ya mika takardar murabus dinsa ga Shugaban Unguwa a Unguwar Dogo-tebo da ke Potiskum.

Waziri, mamban kwamitin amintattu na PDP, ya yi nuni da cewa “jagoranci da alkiblar PDP a halin yanzu bai dace da babbar jam’iyyar siyasa ba,” ya kara da cewa jam’iyyar “ta rasa matsayinta na ‘yan adawa na farko.”

Ya yi alkawarin tattara abokansa na siyasa don shiga ADC, yana mai kira ga wasu da su shiga cikin wani yunkuri na maido da fata na dimokradiyya a kasar.

Ficewar Waziri ya zo daidai da taron jam’iyyar ADC na shiyyar Potiskum a garin Potiskum, inda shugabannin jam’iyyar suka yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga matasa da mata da tsofaffi da su shiga jam’iyyar ADC domin ciyar da kasa gaba.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp