Tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai, Lasun Yusuf ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki.
Yusuf ya mika takardar murabus din sa ne a sakatariyar jam’iyyar ta jihar Osun, Osogbo da safiyar Juma’a.
Duk da cewa ,har yanzu ba a bayyana cikakken bayanin wasikar ba, wani jami’in jam’iyyar ya tabbatar da cewa, Lasun ya yi murabus daga mukaminsa.
Yusuf ya kasance tsohon dan takarar gwamna a jam’iyyar APC a 2018.
Ya kuma yi burin zama dan takarar gwamna a jam’iyyar a zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka kammala kwanan nan.