fidelitybank

Tsohon mataimakin gwamnan Neja ya koma APC daga PDP

Date:

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Neja kuma tsohon jakadan Najeriya a kasar Afrika ta kudu, Ahmed Musa Ibeto da wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP guda biyu sun fice daga jam’iyyar sun koma jam’iyyar APC mai mulki.

Ibrahim Egbo, tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Lapai Agaie na tarayya da Alhaji Abubakar Azozo, tsohon kwamishinan albarkatun ruwa na jihar Neja, sune sauran jiga-jigan siyasar biyu da suka bar PDP zuwa APC.

Ibeto, wanda ya gabatar da kansa da sauran biyun a sakatariyar jam’iyyar APC ta jihar da ke Minna, ya dogara ne da irin salon jagorancin Gwamna Mohammed Umar Bago.

“APC ce gida na kuma na dawo gida. Akwai wasu mutane da dama da suka hada da mabiyansu daga wasu jam’iyyun siyasa da ke kan hanyarsu ta zuwa APC,” ya bayyana.

Da aka tambaye shi ko kudiri ne ko nadin siyasa ya sa Ibeto ya ce: “Na yanke shawarar ne a kan hukuncin da na yanke saboda duk matsalolin da suka tilasta ni ficewa daga APC a baya babu su a gwamnatin Mohammed Umar Bago.”

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alh Aminu Musa Bobi, ya kara bayyana cewa jam’iyyar ta fara tattara bayanan duk masu rike da mukaman siyasa a jihar domin su kasance masu rikon amana da kuma isa ga jama’arsu a matakin farko.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp