fidelitybank

Tsohon mataimakin gwamnan Neja ya koma APC daga PDP

Date:

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Neja kuma tsohon jakadan Najeriya a kasar Afrika ta kudu, Ahmed Musa Ibeto da wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP guda biyu sun fice daga jam’iyyar sun koma jam’iyyar APC mai mulki.

Ibrahim Egbo, tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Lapai Agaie na tarayya da Alhaji Abubakar Azozo, tsohon kwamishinan albarkatun ruwa na jihar Neja, sune sauran jiga-jigan siyasar biyu da suka bar PDP zuwa APC.

Ibeto, wanda ya gabatar da kansa da sauran biyun a sakatariyar jam’iyyar APC ta jihar da ke Minna, ya dogara ne da irin salon jagorancin Gwamna Mohammed Umar Bago.

“APC ce gida na kuma na dawo gida. Akwai wasu mutane da dama da suka hada da mabiyansu daga wasu jam’iyyun siyasa da ke kan hanyarsu ta zuwa APC,” ya bayyana.

Da aka tambaye shi ko kudiri ne ko nadin siyasa ya sa Ibeto ya ce: “Na yanke shawarar ne a kan hukuncin da na yanke saboda duk matsalolin da suka tilasta ni ficewa daga APC a baya babu su a gwamnatin Mohammed Umar Bago.”

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alh Aminu Musa Bobi, ya kara bayyana cewa jam’iyyar ta fara tattara bayanan duk masu rike da mukaman siyasa a jihar domin su kasance masu rikon amana da kuma isa ga jama’arsu a matakin farko.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp