Tsohon mataimakin gwamnan jihar Neja kuma tsohon jakadan Najeriya a kasar Afrika ta kudu, Ahmed Musa Ibeto da wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP guda biyu sun fice daga jam’iyyar sun koma jam’iyyar APC mai mulki.
Ibrahim Egbo, tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Lapai Agaie na tarayya da Alhaji Abubakar Azozo, tsohon kwamishinan albarkatun ruwa na jihar Neja, sune sauran jiga-jigan siyasar biyu da suka bar PDP zuwa APC.
Ibeto, wanda ya gabatar da kansa da sauran biyun a sakatariyar jam’iyyar APC ta jihar da ke Minna, ya dogara ne da irin salon jagorancin Gwamna Mohammed Umar Bago.
“APC ce gida na kuma na dawo gida. Akwai wasu mutane da dama da suka hada da mabiyansu daga wasu jam’iyyun siyasa da ke kan hanyarsu ta zuwa APC,” ya bayyana.
Da aka tambaye shi ko kudiri ne ko nadin siyasa ya sa Ibeto ya ce: “Na yanke shawarar ne a kan hukuncin da na yanke saboda duk matsalolin da suka tilasta ni ficewa daga APC a baya babu su a gwamnatin Mohammed Umar Bago.”
Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alh Aminu Musa Bobi, ya kara bayyana cewa jam’iyyar ta fara tattara bayanan duk masu rike da mukaman siyasa a jihar domin su kasance masu rikon amana da kuma isa ga jama’arsu a matakin farko.