Tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa kuma daya daga cikin masu neman takarar gwamna a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a 2023, Ahmed Mahmoud Gumel ya fice daga jam’iyyar APC.
Hakan na kunshe ne a cikin wasikar takardar murabus dinsa da ya aike wa manema labarai.
Takardar dai na dauke da sa hannun tsohon mataimakin gwamnan ne kuma ta aikewa shugaban jam’iyyar APC ward Galangamawa a karamar hukumar Gumel.
A cewar wasikar “Tare da dukkan mutuntawa da girmamawa a matsayin shugaba, mutuminka da jam’iyyarka su sanar da kai murabus na daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
“An tilasta min daukar wannan matakin ne saboda bayyananniyar rikicin cikin jam’iyya, rashin hadin kai da rashin jajircewa da kuma kwarin gwiwa ga jiga-jigan jam’iyyar wajen samun nasarar jam’iyyar a babban zabe mai zuwa.
Ahmed Gumel ya tabbatar wa jam’iyyar APC ci gaba da tuntubar masu ruwa da tsaki na jam’iyyar kan duk wani shiri na gaba, ya kuma yi wa daukacin ‘ya’yan jam’iyyar fatan alheri a harkokinsu na yau da gobe.
Ahmed ya taba rike mukamin kwamishinan kudi a zamanin gwamnatin tsohon Gwamna Ibrahim Saminu Turaki. Ya kuma taba zama mataimakin gwamna a karkashin tsohon Gwamna Sule Lamido a tsarin jam’iyyar PDP.
Ya fice daga PDP watanni kadan kafin zaben 2015 na jam’iyyar All Progressives Congress, APC.