Tsohon Jakadan Najeriya a kasar Jordan kuma jigo a jam’iyyar APC, Faruk Malami Yabo ,ya fice daga jam’iyyar APC ya rungumi jam’iyyar PDP a jihar Sokoto.
Tsohon Jakadan ya bayyana aniyarsa ta komawa jam’iyyar PDP ne a yayin taron yakin neman zaben jam’iyyar a garin Yabo da ke karamar hukumar Yabo, inda ya ce komawarsa PDP gida ne.
“PDP ta kasance jam’iyyata kuma komawata jam’iyya na iya dangantawa da labarin dan fajirci.”
Ya godewa jama’ar da ke cikin tafiyar, inda ya yi alkawarin yin duk abin da zai iya domin ganin jam’iyyar PDP ta samu nasara a jihar.
Da yake mayar da martani, gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya bayyana sauya shekar Yabo a matsayin abin farin ciki.
Gwamna Tambuwal ya yabawa tsohon Ambasada bisa hikimar da ya yanke na komawa jam’iyyar, inda ya ce ya dauki wannan matakin ne domin amfanin jam’iyyar da kuma al’ummar jihar.