Rahotanni sun bayyana cewa tsohon hadimin shugaban kasa, Dr. Doyin Okupe ya mutu.
Fitaccen dan siyasar Najeriya ya rasu yana da shekaru 72 a duniya.
An tattaro cewa Dr. Okupe ya mutu ne da safiyar Juma’a bayan ya yi fama da doguwar jinya da ake zargin ciwon daji ne.
A shekarar 2022 ne aka nada Okupe a matsayin Darakta-Janar na yakin neman zaben Shugaban kasa na Jam’iyyar Labour a zaben 2023.
Sai dai kuma an tilasta masa yin murabus ne bayan da kotu ta yanke masa hukunci kan zargin karkatar da kudade.
A cewar majiyoyin da ke kusa da dangin, Okupe ya yi fama da rashin lafiya a makonnin da suka rage kafin rasuwarsa.