fidelitybank

Tsohon hadimin Buhari ya shawarci Tinubu a kan shawarar IMF

Date:

Tsohon shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa na tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, farfesa Ibrahim Gambari, ya gargaɗi gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta su riƙa yin taka-tsantsan wajen amfani da shawarwarin bankin duniya da bankin lamuni na duniya wato IMF.

Gambari ya ce, “mene ne amfanin tsare-tsaren gwamnati idan mutane ba sa so?” in ji shi a tattaunawarsa da tashar Channels.

“Bankin duniya da IMF abokan hulɗarmu ne, don haka idan suka kawo mana wasu shawarwari, sai muka ga ba za su ɓille mana ba, sai mu gyara su domin su dace da tsarinmu, saboda jin daɗin mutanenmu da ci gaban ƙasarmu ne a gaba da komai.”

Farfesa Gambari ya ƙara da cewa Najeriya ta ci sa’a, “saboda da wasu ƙasashen ne rayuwa ta yi tsada haka, da zanga-zanga ce za ta ɓarke. Ƴan Najeriya ba sa damuwa kan neman abubuwa masu yawa daga gwamnati, shi ya sa kowa ya cigaba da gudanar da harkokinsa. A ƙasashe irin su Sudan, farashin burodi ne ya ƙaru da kashi 20, amma zanga-zange ta ɓarke wanda ta rikiɗe zuwa tarzoma. Amma a Najeriya mutane suna gyara zama ne kawai su cigaba da harkokinsu. Amma ya kamata mu ɗauki matakin da ya dace, ba sai an yi juyin juya hali ba.”

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp