Tsohon shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa na tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, farfesa Ibrahim Gambari, ya gargaɗi gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta su riƙa yin taka-tsantsan wajen amfani da shawarwarin bankin duniya da bankin lamuni na duniya wato IMF.
Gambari ya ce, “mene ne amfanin tsare-tsaren gwamnati idan mutane ba sa so?” in ji shi a tattaunawarsa da tashar Channels.
“Bankin duniya da IMF abokan hulɗarmu ne, don haka idan suka kawo mana wasu shawarwari, sai muka ga ba za su ɓille mana ba, sai mu gyara su domin su dace da tsarinmu, saboda jin daɗin mutanenmu da ci gaban ƙasarmu ne a gaba da komai.”
Farfesa Gambari ya ƙara da cewa Najeriya ta ci sa’a, “saboda da wasu ƙasashen ne rayuwa ta yi tsada haka, da zanga-zanga ce za ta ɓarke. Ƴan Najeriya ba sa damuwa kan neman abubuwa masu yawa daga gwamnati, shi ya sa kowa ya cigaba da gudanar da harkokinsa. A ƙasashe irin su Sudan, farashin burodi ne ya ƙaru da kashi 20, amma zanga-zange ta ɓarke wanda ta rikiɗe zuwa tarzoma. Amma a Najeriya mutane suna gyara zama ne kawai su cigaba da harkokinsu. Amma ya kamata mu ɗauki matakin da ya dace, ba sai an yi juyin juya hali ba.”