Tsohon mai taimaka wa shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a kafafen sada zumunta na zamani, Malam Bashir Ahmad, ya bayar da tallafin karatu ga wata mai hazaka da ba ta zuwa makaranta, Saratu Dan-Azumi, tun daga firamare har zuwa jami’a.
Bidiyon yarinyar da ke nuna gwaninta a fannin lissafi, ta hanyar ba da amsa ga kowane tambaya kan lissafi kwanan nan ya karade ko ina.
Jama’a da dama ne suka fito a dandalinsu na sada zumunta inda suka nuna farin cikinsu, bisa hikimar wata matashiya Saratu da ke zaune a kauyen Gwadayi da ke unguwar Shagogo a karamar hukumar Gaya a jihar Kano.
Sai dai da zarar ya karbi faifan bidiyon, tsohon mataimaki, wanda ya tsaya takarar tikitin takarar kujerar majalisar wakilai a zaben fidda gwanin da ya gabata a dandalin jam’iyyar All Progressives Congress, ya fara neman yarinyar.
Ta gidauniyar Bashir Ahmad Foundation, an gano yarinyar kuma an ba ta tallafin ne, bisa yardar iyayenta da hakimin garinsu.
“Bayan na karbi faifan bidiyon yarinyar mai hazaka daga mutane daban-daban, na aika da wata tawaga ta gidauniyata domin nemanta kuma aka yi sa’a aka same ta. Mun amince da iyayenta kuma za mu dauki nauyin karatun ta zuwa Jami’a.
“Mun riga mun zabo mata makaranta kuma ranar Litinin za a shigar da ita makarantar firamare. Bayan haka za mu ci gaba da kula da karatun ta da kuma tabbatar da mun cika alkawuran da muka dauka,” ya rubuta a shafinsa na Facebook.
Ya kara da cewa, baya ga tallafawa karatun ta, gidauniyar za ta shigar da ita cibiyar Gaya Digital Centre, inda za ta samu ilimi a fannin fasahar sadarwa.