fidelitybank

Tsohon hadimin Buhari ya dauki nauyin karatun yarinya tun daga Firamare har zuwa Jami’a

Date:

Tsohon mai taimaka wa shugaban kasa, Muhammadu Buhari, a kafafen sada zumunta na zamani, Malam Bashir Ahmad, ya bayar da tallafin karatu ga wata mai hazaka da ba ta zuwa makaranta, Saratu Dan-Azumi, tun daga firamare har zuwa jami’a.

Bidiyon yarinyar da ke nuna gwaninta a fannin lissafi, ta hanyar ba da amsa ga kowane tambaya kan lissafi kwanan nan ya karade ko ina.

Jama’a da dama ne suka fito a dandalinsu na sada zumunta inda suka nuna farin cikinsu, bisa hikimar wata matashiya Saratu da ke zaune a kauyen Gwadayi da ke unguwar Shagogo a karamar hukumar Gaya a jihar Kano.

Sai dai da zarar ya karbi faifan bidiyon, tsohon mataimaki, wanda ya tsaya takarar tikitin takarar kujerar majalisar wakilai a zaben fidda gwanin da ya gabata a dandalin jam’iyyar All Progressives Congress, ya fara neman yarinyar.

Ta gidauniyar Bashir Ahmad Foundation, an gano yarinyar kuma an ba ta tallafin ne, bisa yardar iyayenta da hakimin garinsu.

“Bayan na karbi faifan bidiyon yarinyar mai hazaka daga mutane daban-daban, na aika da wata tawaga ta gidauniyata domin nemanta kuma aka yi sa’a aka same ta. Mun amince da iyayenta kuma za mu dauki nauyin karatun ta zuwa Jami’a.

“Mun riga mun zabo mata makaranta kuma ranar Litinin za a shigar da ita makarantar firamare. Bayan haka za mu ci gaba da kula da karatun ta da kuma tabbatar da mun cika alkawuran da muka dauka,” ya rubuta a shafinsa na Facebook.
Ya kara da cewa, baya ga tallafawa karatun ta, gidauniyar za ta shigar da ita cibiyar Gaya Digital Centre, inda za ta samu ilimi a fannin fasahar sadarwa.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp