Ministan harkokin Neja Delta, Godswill Akpabio ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom, ya bayyana hakan ne a yau Laraba, 4 ga watan Mayu, 2022, a gaban dimbin magoya bayan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a babban filin wasa na garin Ikot Ekpene.
Akpabio zai fafata da irin su mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo; Bola Tinubu, tsohon gwamnan Legas; Rotimi Amaechi, ministan sufuri, da Yahaya Bello, gwamnan Kogi; da sauransu don tikitin.