Jami’an hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya, sun kama tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel bisa zargin almundanar naira biliyan 700.
An kama Mista Emmanuel bayan ya amsa gayyatar hukumar a ranar Talata domin amsa wasu tambayoyi kan zargin karkatar da kuɗi da wata ƙungiya mai rajin yaƙi da cin hanci ta yi masa.
Ƙungiyar ta zargi tsohon gwamnan ta karɓar naira tiriliyan uku daga asusun gwamnatin tarayya a tsawon shekara takwas da ya yi yana mulki, amma ya bar wa jihar bashin naira biliyan 500 da rashin biyan kuɗin wasu ayyuka na naira biliyan 300 bayan ya sauka.
Haka kuma ƙungiyar ta zargi Mista Emmanuel da kasa yin bayani kan yadda aka kashe wasu maƙudan kuɗi har naira biliyan 700, kamar yadda gidan talbijin na Channels ta ruwaito.
Emmanuel ya kasance gwamnan jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya daga 2015 zuwa 2023, ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
A ranar Juma’ar da ta gabata ma da hukumar EFCC ta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Abia, Theodore Orji da wasu mutum huɗu a gaban kotu, bisa zargin ɓarnatar da kusan naira biliyan 47.