Daruruwan shugabannin jam’iyya da magoya bayansa ne suka yi dafifi a sakatariyar jam’iyyar APC ta Adamawa yayin da tsohon gwamnan jihar, Mohammed Umaru Jibrilla Bindow ya bayyana aniyarsa ta shiga takarar gwamna.
Sanata Jibrilla Bindow, tsohon gwamnan Adamawa da ya shiga takarar gwamna a jihar a karkashin jam’iyyar APC, ya ja hankalin jama’a da dama a wurin domin shaida yadda ya bayyana.
Bindow ya ce, zai gyara tattalin arzikin kasar, tare da mika ribar dimokuradiyya ga daukacin al’ummar jihar Adamawa.
Ya kuma ce, a karshe ya yanke shawarar sake tsayawa takara, domin ya kammala wa’adinsa na biyu a mulki.
Ya kara da cewa, duk masu neman takarar gwamna a jam’iyyar APC sun cancanta; inda ya bukace su da su ba shi dama ya ci gaba daga inda ya tsaya, domin ci gaba da ceto al’umma daga matsanancin talauci.
Bindow ya yi kira ga masu zabe da su ba shi damar yiwa jihar hidima a karo na biyu.
“Na yi abubuwa da yawa a jihar lokacin da nake Gwamna, kuma ina da tsare-tsare da dama a jihar, amma mun fadi zabe a 2019 saboda rigingimu, amma da fatan idan aka sake zaɓa ta a 2023, zan firgita jama’a ta hanyar samar da dimbin arziki da ci gaba”. In ji Bindow
A nasa jawabin shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Ibrahim Bilal ya bukaci hadin kan jam’iyyar.
Ya shawarci duk masu son yin aiki tare da juna domin cimma manufa daya ta lashe jihar a 2023.
Bindow ya bayyana cewa, fahimtar juna da hadin kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar na da matukar muhimmanci ga ci gaban jam’iyyar gabanin zaben 2023 mai zuwa.
An zabi Bindow a matsayin gwamnan jihar Adamawa a shekara ta 2015 kafin ya fadi zabe a karo na biyu a 2019.