fidelitybank

Tsohon Firaministan Japan Shinzo Abe ya mutu

Date:

Tsohon firaministan Japan, Shinzo Abe ya rasu, kamar yadda kafar yada labaran kasar ta sanar.

An harbi Abe mai shekara 67 ne a yayin da yake jawabi a wajen wani gangamin yakin neman zabe.

An harbi Mista Abe sau biyu a yayin da yake gabatar da jawabi a birnin Nara ranar Juma’a da safe.

Ba a bata lokaci ba aka garzaya da tsohon fira ministan mai shekara 67 asibiti. Wakilin BBC ya ce harbi na farko bai same shi ba, to amma harbi na biyu an sami Mr Abe a baya, kuma nan take ya yanke jiki ya fadi kasa cikin jini.

Wata majiya daga ‘yan sanda ta ce an kama wani mutum da ake zargi da harbin.

Tsohon Gwamnan Tokyo Yoichi Masuzoe cikin wani sakon Twitter ya ce Mista an harbi Mista Abe da misalin karfe 11:30 agogon Japan.

Mista Abe na yin wani jawabin tallata wani dan takara ne, yayin wani gangamin yakin neman zabe a nara lokacin da harin ya auku – kuma shaidu sun ga wani mutum dauke da wata babbar bindiga kuma sun ce ya harbe Mista Abe a bayansa.

Mista Abe ne firaministan da ya fi dadewa kan karagar mulki.

Ya fara zama firaminista a 2006 na shekara guda, kuma daga baya ya rike mukamin daga 2012 zuwa 2020, sai dai ya sauka da kansa domin matsalolin rashin lafiya.

Ba kasafai a ke kai irin wannan hari da bindiga ba a Japan, kasar da aka hana mutane mallakar bindigogi sannan ba a cika jin labarin hare-hare a dalilai na siyasa ba a kasar. In ji BB

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...
X whatsapp