Tsohon firaministan Japan, Shinzo Abe ya rasu, kamar yadda kafar yada labaran kasar ta sanar.
An harbi Abe mai shekara 67 ne a yayin da yake jawabi a wajen wani gangamin yakin neman zabe.
An harbi Mista Abe sau biyu a yayin da yake gabatar da jawabi a birnin Nara ranar Juma’a da safe.
Ba a bata lokaci ba aka garzaya da tsohon fira ministan mai shekara 67 asibiti. Wakilin BBC ya ce harbi na farko bai same shi ba, to amma harbi na biyu an sami Mr Abe a baya, kuma nan take ya yanke jiki ya fadi kasa cikin jini.
Wata majiya daga ‘yan sanda ta ce an kama wani mutum da ake zargi da harbin.
Tsohon Gwamnan Tokyo Yoichi Masuzoe cikin wani sakon Twitter ya ce Mista an harbi Mista Abe da misalin karfe 11:30 agogon Japan.
Mista Abe na yin wani jawabin tallata wani dan takara ne, yayin wani gangamin yakin neman zabe a nara lokacin da harin ya auku – kuma shaidu sun ga wani mutum dauke da wata babbar bindiga kuma sun ce ya harbe Mista Abe a bayansa.
Mista Abe ne firaministan da ya fi dadewa kan karagar mulki.
Ya fara zama firaminista a 2006 na shekara guda, kuma daga baya ya rike mukamin daga 2012 zuwa 2020, sai dai ya sauka da kansa domin matsalolin rashin lafiya.
Ba kasafai a ke kai irin wannan hari da bindiga ba a Japan, kasar da aka hana mutane mallakar bindigogi sannan ba a cika jin labarin hare-hare a dalilai na siyasa ba a kasar. In ji BB