fidelitybank

Tsohon dan wasan Chelsea ya na cikin wanda gini ya danne a Turkiyya

Date:

An kuɓutar da ɗan wasan ƙwallon ƙafar Ghana Christian Atsu daga cikin ɓaraguzan da ya maƙale sakamakon girgizar ƙasar da ta afka wa wasu yankunan Turkiyya.

Dan wasan ya samu raunuka bayan ginin da yake ciki ya rufta a yankin Hayat na Turkiyya, kamar yadda manajansa ya shaida wa gidan radiyon Turkiyya.

Tun da farko dai Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ghana ta buƙaci magoya bayan ƙwallon ƙafa a ƙasar da su sanya ɗan wasan cikin addu’o’insu.

Karanta Wannan: Chelsea ta dauki dan wasan bayan Lyon

Rahotonni sun ce ɗan wasan tare da daraktan ƙungiyarsa sun maƙale ne cikin ɓaraguzan gine-gine sakamakon mummunar girgizar ƙasar da ta afka wa wasu yankunan Turkiyya da Siriya.

Hatayspor ita ce babbar ƙungiyar ƙwallon a yankin Hayat, ɗaya daga cikin biranen da girgizar ƙasar mai ƙarfin maki 7.5 ta shafa.

Rahotonni sun ce girgizar ƙasar ta yi sanadin mutuwar sama da mutum 4000 a Turkiya da Siriya.

Hukumar Ƙwallon ƙafar Ghana ta wallafa a shafinta na Tuwita cewa ”Muna addu’a ga ɗan wasan Ghana Christian Atsu da sauran mutanen da girgizar ƙasar ta shafa a Turkiya da Siriya.”

Ita ma tsohuwar ƙungiyarsa ta Newcastle a wani saƙon Tuwita da ta wallafa ta yi addu’ar samun kuɓuta ga ɗan wasan.

Atsu, wanda ya buga wa Ghana wasanni 65, ya ɗauki lokaci mai tsawo yana taka-leda a ƙungiyoyin Ingila inda a shekarar 2013 ya sanya hannu da ƙungiyar Chelsea.

Haka kuma ya yi wasanni a ƙungiyoyin Everton da Bournemouth da kuma Newcastle United.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp