An kuɓutar da ɗan wasan ƙwallon ƙafar Ghana Christian Atsu daga cikin ɓaraguzan da ya maƙale sakamakon girgizar ƙasar da ta afka wa wasu yankunan Turkiyya.
Dan wasan ya samu raunuka bayan ginin da yake ciki ya rufta a yankin Hayat na Turkiyya, kamar yadda manajansa ya shaida wa gidan radiyon Turkiyya.
Tun da farko dai Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ghana ta buƙaci magoya bayan ƙwallon ƙafa a ƙasar da su sanya ɗan wasan cikin addu’o’insu.
Karanta Wannan: Chelsea ta dauki dan wasan bayan Lyon
Rahotonni sun ce ɗan wasan tare da daraktan ƙungiyarsa sun maƙale ne cikin ɓaraguzan gine-gine sakamakon mummunar girgizar ƙasar da ta afka wa wasu yankunan Turkiyya da Siriya.
Hatayspor ita ce babbar ƙungiyar ƙwallon a yankin Hayat, ɗaya daga cikin biranen da girgizar ƙasar mai ƙarfin maki 7.5 ta shafa.
Rahotonni sun ce girgizar ƙasar ta yi sanadin mutuwar sama da mutum 4000 a Turkiya da Siriya.
Hukumar Ƙwallon ƙafar Ghana ta wallafa a shafinta na Tuwita cewa ”Muna addu’a ga ɗan wasan Ghana Christian Atsu da sauran mutanen da girgizar ƙasar ta shafa a Turkiya da Siriya.”
Ita ma tsohuwar ƙungiyarsa ta Newcastle a wani saƙon Tuwita da ta wallafa ta yi addu’ar samun kuɓuta ga ɗan wasan.
Atsu, wanda ya buga wa Ghana wasanni 65, ya ɗauki lokaci mai tsawo yana taka-leda a ƙungiyoyin Ingila inda a shekarar 2013 ya sanya hannu da ƙungiyar Chelsea.
Haka kuma ya yi wasanni a ƙungiyoyin Everton da Bournemouth da kuma Newcastle United.