Tsohon dan majalisar wakilai daga jihar Kogi, Hon. Mohammed Idris, ya rasu.
Mohammed, dan tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Ibrahim Idris, ya wakilci mazabar Ankpa, Olamaboro da kuma Omala a zauren majalisar dokokin kasar.
DAILY POST ta tattaro cewa ya fadi ya mutu jim kadan bayan kammala Sallar Idi a gidansa da ke Abuja ranar Laraba.
Za a yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a makabartar Gudu da ke Abuja.