Dennis Amachree, mataimakin daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) mai ritaya, ya shawarci ‘yan Najeriya da su nemi sabon shugabancin da zai baiwa Najeriya sabuwar alkibla
Ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su yi fatali da sake amfani da shugabanni, wadanda iyalansu suka kwashe shekaru suna fagen siyasa, kuma ba su da wani abin da za su iya nunawa, don haka sabuwar Najeriyar da ake fata ba za ta iya fitowa ba.
Da yake jawabi a matsayin bako mai jawabi a taron shekara-shekara na Afrikanwatch Network mai taken, “Sabuwar Najeriya, mai akidar kirkire-kirkire, maras shugabanni munafukai”, a Legas, ya bayyana cewa, ‘yan siyasar kasar nan ba su da akidar haifar da sabuwar kasa.
Ya koka da cewa, tun bayan samun ‘yancin kai, “A ambaci shugaban kasa daya da ya jagoranci kasar nan a zahiri, kuma ka yi tunanin yawan masu mulkin Najeriya, a matakin shugaban kasa, tun bayan samun ‘yancin kai.