fidelitybank

Tsofaffin Kwamishinonin Ganduje biyu sun rasu

Date:

Tsofaffin kwamishinoni biyu a jihar Kano, wadanda suka yi aiki a tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje, sun rasu.

Tsofaffin Kwamishinonin biyu, Alhassan Muhammad Dawaki da Barista Zubaida Damakka wadanda suka kasance kwamishinonin kananan hukumomi da masarautu da kuma kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, sun rasu ne a ranar Juma’a.

Alhassan Muhammad Dawaki, a cewar wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shu’aibu ya fitar, ya rasu ne bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya yana da shekaru 79 kuma ya bar mata da ‘ya’ya 15.

Tsohon babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan kafafen sadarwa na zamani, Abubakar Aminu Ibrahim, ya tabbatar da rasuwar Barista Zubaida Damakka, inda ya ce ta rasu ne a Abuja bayan gajeruwar rashin lafiya, ta bar ‘ya’ya uku da miji.

An yi Sallar Jana’izar su a Kano ranar Lahadi kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Sanarwar ta bayyana Dawaki a matsayin wani fitaccen mutumi kuma mutuniyar da ake mutuntawa wanda tafiyar kwatsam ta bar wani gibi a zukatan mutane da dama.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi na’am da gagarumin rashi da rasuwar Dawaki ta yi a lokacin da yake gabatar da addu’o’in samun karfin gwuiwa da juriya ga ‘yan uwa da ke cikin makoki, yana mai yi musu fatan Alheri a cikin mawuyacin hali na makoki.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp