Tsofaffin kwamishinoni biyu a jihar Kano, wadanda suka yi aiki a tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje, sun rasu.
Tsofaffin Kwamishinonin biyu, Alhassan Muhammad Dawaki da Barista Zubaida Damakka wadanda suka kasance kwamishinonin kananan hukumomi da masarautu da kuma kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, sun rasu ne a ranar Juma’a.
Alhassan Muhammad Dawaki, a cewar wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shu’aibu ya fitar, ya rasu ne bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya yana da shekaru 79 kuma ya bar mata da ‘ya’ya 15.
Tsohon babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan kafafen sadarwa na zamani, Abubakar Aminu Ibrahim, ya tabbatar da rasuwar Barista Zubaida Damakka, inda ya ce ta rasu ne a Abuja bayan gajeruwar rashin lafiya, ta bar ‘ya’ya uku da miji.
An yi Sallar Jana’izar su a Kano ranar Lahadi kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Sanarwar ta bayyana Dawaki a matsayin wani fitaccen mutumi kuma mutuniyar da ake mutuntawa wanda tafiyar kwatsam ta bar wani gibi a zukatan mutane da dama.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi na’am da gagarumin rashi da rasuwar Dawaki ta yi a lokacin da yake gabatar da addu’o’in samun karfin gwuiwa da juriya ga ‘yan uwa da ke cikin makoki, yana mai yi musu fatan Alheri a cikin mawuyacin hali na makoki.