fidelitybank

Tsofaffin Kwamishinonin Ganduje biyu sun rasu

Date:

Tsofaffin kwamishinoni biyu a jihar Kano, wadanda suka yi aiki a tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje, sun rasu.

Tsofaffin Kwamishinonin biyu, Alhassan Muhammad Dawaki da Barista Zubaida Damakka wadanda suka kasance kwamishinonin kananan hukumomi da masarautu da kuma kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, sun rasu ne a ranar Juma’a.

Alhassan Muhammad Dawaki, a cewar wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shu’aibu ya fitar, ya rasu ne bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya yana da shekaru 79 kuma ya bar mata da ‘ya’ya 15.

Tsohon babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan kafafen sadarwa na zamani, Abubakar Aminu Ibrahim, ya tabbatar da rasuwar Barista Zubaida Damakka, inda ya ce ta rasu ne a Abuja bayan gajeruwar rashin lafiya, ta bar ‘ya’ya uku da miji.

An yi Sallar Jana’izar su a Kano ranar Lahadi kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Sanarwar ta bayyana Dawaki a matsayin wani fitaccen mutumi kuma mutuniyar da ake mutuntawa wanda tafiyar kwatsam ta bar wani gibi a zukatan mutane da dama.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi na’am da gagarumin rashi da rasuwar Dawaki ta yi a lokacin da yake gabatar da addu’o’in samun karfin gwuiwa da juriya ga ‘yan uwa da ke cikin makoki, yana mai yi musu fatan Alheri a cikin mawuyacin hali na makoki.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...
X whatsapp