fidelitybank

Tsige shugaban PDP tamkar wani annoba ne – Melaye

Date:

Tsohon dan majalisa mai wakiltan Kogi ta Yamma, Sanata Dino Melaye ya yi gargadi game da tsige shugaban jam’iyyar na kasa, Iyorchia Ayu ba bisa ka’ida ba gabanin zaben shugaban kasa na 2023.

Melaye, wanda ya yi wannan gargadin a lokacin da yake gabatar da tambayoyi daga DAILY POST a yayin bikin cika shekaru 75 na Sanata Tunde Ogbeha, ya ce, tsige Ayu da gwamnan jihar River, Nyesom Wike ke yi zai haifar da rikicin tsarin mulki a jam’iyyar.

Yayin da yake bayyana Gwamna Wike a matsayin dan Najeriya mai kishin kasa wanda nan ba da dadewa ba zai cika shekaru 60, Melaye ya bayyana cewa fitowar Ayu a matsayin Shugaban PDP na kasa yana samun goyon bayan Gwamnonin PDP ciki har da Wike.

Ya ce cire Ayu kamar zubar da ciki ne a PDP kafin sakamakon zaben shugaban kasa na 2023.

Melaye ya ce “Na kasance a wurin taron ne lokacin da ya yi wa ‘yan Najeriya alkawari a gidan talabijin na kasa cewa duk wanda ya fito a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP, zai goyi bayan mutumin. Har yanzu na tsaya a kan haka domin shi mutum ne mai gaskiya kuma ban gan shi yana cin maganarsa ba.

“Don haka duk abin da kuka gani, yana faruwa ne sakamakon firamare. Ya zama al’ada bayan duk wani zaben fidda gwanin za a yi ta tada zaune tsaye da korafe-korafe amma wadannan ba abubuwa ne da suka isa su raba kan jam’iyyar ba.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp