Ɗan majalisar dokokin Legas mai wakiltar mazaɓar Agege a jihar Legas, Mudashiru Obasa ya ce ya koma bakin aiki a matsayin shugaban majalisar.
Obasa ya bayyana haka ne a lokacin da ya shiga zauren majalisar a yau Alhamis.
Lokacin da aka tambaye shi game da tsigewar da aka masa, Obasa ya ce “Babu wanda ya tsige ni. Batun tsigewa ko ma mene ne abu ne da ke buƙatar a bi doka.”
Sai dai wasu daga cikin ƴan majalisar masu goyon bayan ƴar majalisar Mojisola Meranda, wadda aka naɗa shugabar majalisar a kwanakin baya, sun yi watsi da batun, inda suka dage kan cewa Meranda ɗin ce shugabar majalisar.
Obasa ya bayyana a harabar Majalisar ne tare da rakiyar jami’an tsaro.
Shigarsa harabar majalisar a yau Alhamis ita ce ta farko yun bayan tsige shi da majalisar ta yi a watan Janairun da ya gabata.