fidelitybank

Tsaro: ‘Yan Najeriya ku hada kai domin kawo karshen ta’addanci

Date:

Mai martaba Sarkin Musulmai, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar na Uku, ya shawarci ‘yan Najeriya da su hada kai, domin kawo karshen ta’addanci a Najeriya.

Sultan ya furta hakan ne a taron majalisar hadin kan addinai ta (NIREC), ya ce ba lokaci ba ne da mabiya addinai musamman Musulmi da Kirista za su rinka zargin juna da yi wa juna barazana ba.

Mai martaba Sultan, ya nuna damuwa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jam’a ke ci gaba da kamari a Najeriya, amma kuma Musulmi da Kirista sun bige da nuna wa juna yatsa da yi wa juna barazana.

Ya kuma ce,”Dole ne mu daina zargin juna, kuma mu hada kai, domin mu yaki makiyan mu, idan na ce zan yi magana kan rashin tsaro a Arewa babu lokacin da za mu bar dakin taron nan”. A cewar Sultan.

Ya kara da cewa, “Yan kwanakin da suka wuce mun karanta a jaridu yadda aka kona matafiya a bas a Sokoto. Babu ranar da za ta zo ta wuce ba a kashe mutane a Arewa ba, musamman Arewa maso Yamma”.

Bugu da kari, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar ya bukaci shugabanni da sauran hukumomin tsaro su hada kai su kuma fahimci girman matsalar tare da magance ta. Inji BBC.

 

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp