Mai martaba Sarkin Musulmai, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar na Uku, ya shawarci ‘yan Najeriya da su hada kai, domin kawo karshen ta’addanci a Najeriya.
Sultan ya furta hakan ne a taron majalisar hadin kan addinai ta (NIREC), ya ce ba lokaci ba ne da mabiya addinai musamman Musulmi da Kirista za su rinka zargin juna da yi wa juna barazana ba.
Mai martaba Sultan, ya nuna damuwa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jam’a ke ci gaba da kamari a Najeriya, amma kuma Musulmi da Kirista sun bige da nuna wa juna yatsa da yi wa juna barazana.
Ya kuma ce,”Dole ne mu daina zargin juna, kuma mu hada kai, domin mu yaki makiyan mu, idan na ce zan yi magana kan rashin tsaro a Arewa babu lokacin da za mu bar dakin taron nan”. A cewar Sultan.
Ya kara da cewa, “Yan kwanakin da suka wuce mun karanta a jaridu yadda aka kona matafiya a bas a Sokoto. Babu ranar da za ta zo ta wuce ba a kashe mutane a Arewa ba, musamman Arewa maso Yamma”.
Bugu da kari, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar ya bukaci shugabanni da sauran hukumomin tsaro su hada kai su kuma fahimci girman matsalar tare da magance ta. Inji BBC.