A ci gaba da nuna damuwa kan yawaitar laifukan fyade, garkuwa da mutane da tabarbarewar ilimi a Arewacin Najeriya, kungiyar matasa a garin Potiskum da ke jihar Yobe, sun gudanar da zanga-zangar lumana suna kira ga hukumomi da su yi abin da ya dace wajen magance matsalolin zamantakewa.
Shugaban kungiyar, Kwamared Aliyu Haruna, a lokacin da yake zantawa da manema labarai, ya bayyana cewa dalilin da ya sa suka gudanar da zanga-zangar shi ne kira ga hukumomin da abin ya shafa su dauki mataki.
“Mun fara wannan zanga-zangar lumana ne kawai saboda tabarbarewar ilimi a Arewa, da kuma gibin tsaro da ake yi wa yara mata matasa, da marasa laifi da marasa galihu, ana yi musu fyade, a bar su ba tare da komai ba,” inji shi.
Matasan da suka gudanar da zanga-zangar na dauke da alluna dauke da rubuce-rubuce kamar su: ‘A daina kashe ‘yan uwa a Arewa; ‘Karshen Satar Mutane, Fyade’ da ‘Dawo da ‘Yan Matanmu’.