Gwamnatin jihar Katsina ta haramta ayyukan kungiyar ‘Yan Sa Kai, Volunteer Group’ ta ‘yan banga, saboda mummunan ayyukan ta’addanci da ke kai ga kisan gilla kan wadanda ba su ji ba. ba su gani ba, da yawaitar sace-sace.
A wata sanarwa da mai baiwa gwamna shawara na musamman kan harkokin tsaro, Alhaji Ahmed Katsina ya fitar ta ce, dokar ta fara aiki ne nan take.
Haka kuma, gwamnatin jihar Katsina, ta amince da ayyukan kungiyar Vigilante ne kawai, wanda ke karkashin kulawa da lura da sa idon ‘yan sanda, sauran hukumomin tsaro da cibiyoyin gargajiya.
Sanarwar ta ce, daga yanzu: “Rundunar ‘yan sandan Najeriya da sauran jami’an tsaro za su yi maganin duk wani mutum ko gungun mutanen da aka samu suna bayyana kansu a matsayin ‘Yansakai ko wani irin suna mai kama da haka a jihar.” A cewar Alhaji Ahmed.