Tun bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ke fuskanci kakkausar suka daga wajen al’umm, a kan harin da ‘yan ta’adda suka kai na kona matafiya 42 kurmus a Sabon Birni da ke Sokoto, a daidai wannan lokacin Buhari ya fusata ya aike da tawagar manyan jami’an tsaro zuwa yankin.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aike da tawaga mai karfi zuwa jihohin Katsina da Sokoto domin dakile ta’addancin da ke ta karuwa.
Cikin wata sanarwar da Buhari ya yi ya ce,”Na aika da wata tawaga ta manyan jami’an tsaro da na leken asiri karkashin jagorancin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya, zuwa jihohin Sokoto da Katsina, a matsayin martani ga karuwar ayyukan ‘yan ta’adda a jihohin biyu”.
“Ina tsammani daga gare su rahoton halin da ake ciki nan da nan da kuma shawarwari game da ayyukan da za a bi, domin magance wannan yanayin. Ba za mu bar wata kafa ba a yunkurin tabbatar da tsaron rayuwar al’ummar Najeriya, a duk inda suke a kasar nan. Duk abin da a ke bukata za a yi shi, har sai an samu cikakkiyar nasara”. A cewar Buhari.
Sauran ‘yan tawagar tsaron sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba, Darakta-Janar na Hukumar DSS, Yusuf Magaji Bichi, Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, Ambasada Ahmed Rufa’i Abubakar da shugaban tsaro Jami’in leken asiri, Manjo Janar Samuel Adebayo.