fidelitybank

Tsaro: Buhari ya tura tawagar manyan jami’an tsaro zuwa Sokoto da Katsina

Date:

Tun bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ke fuskanci kakkausar suka daga wajen al’umm, a kan harin da ‘yan ta’adda suka kai na kona matafiya 42 kurmus a Sabon Birni da ke Sokoto, a daidai wannan lokacin Buhari ya fusata ya aike da tawagar manyan jami’an tsaro zuwa yankin.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aike da tawaga mai karfi zuwa jihohin Katsina da Sokoto domin dakile ta’addancin da ke ta karuwa.

Cikin wata sanarwar da Buhari ya yi ya ce,”Na aika da wata tawaga ta manyan jami’an tsaro da na leken asiri karkashin jagorancin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya, zuwa jihohin Sokoto da Katsina, a matsayin martani ga karuwar ayyukan ‘yan ta’adda a jihohin biyu”.

“Ina tsammani daga gare su rahoton halin da ake ciki nan da nan da kuma shawarwari game da ayyukan da za a bi, domin magance wannan yanayin. Ba za mu bar wata kafa ba a yunkurin tabbatar da tsaron rayuwar al’ummar Najeriya, a duk inda suke a kasar nan. Duk abin da a ke bukata za a yi shi, har sai an samu cikakkiyar nasara”. A cewar Buhari.

Sauran ‘yan tawagar tsaron sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba, Darakta-Janar na Hukumar DSS, Yusuf Magaji Bichi, Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, Ambasada Ahmed Rufa’i Abubakar da shugaban tsaro Jami’in leken asiri, Manjo Janar Samuel Adebayo.

 

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp