fidelitybank

Tsaro: Buhari ya tura tawagar manyan jami’an tsaro zuwa Sokoto da Katsina

Date:

Tun bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ke fuskanci kakkausar suka daga wajen al’umm, a kan harin da ‘yan ta’adda suka kai na kona matafiya 42 kurmus a Sabon Birni da ke Sokoto, a daidai wannan lokacin Buhari ya fusata ya aike da tawagar manyan jami’an tsaro zuwa yankin.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aike da tawaga mai karfi zuwa jihohin Katsina da Sokoto domin dakile ta’addancin da ke ta karuwa.

Cikin wata sanarwar da Buhari ya yi ya ce,”Na aika da wata tawaga ta manyan jami’an tsaro da na leken asiri karkashin jagorancin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno mai ritaya, zuwa jihohin Sokoto da Katsina, a matsayin martani ga karuwar ayyukan ‘yan ta’adda a jihohin biyu”.

“Ina tsammani daga gare su rahoton halin da ake ciki nan da nan da kuma shawarwari game da ayyukan da za a bi, domin magance wannan yanayin. Ba za mu bar wata kafa ba a yunkurin tabbatar da tsaron rayuwar al’ummar Najeriya, a duk inda suke a kasar nan. Duk abin da a ke bukata za a yi shi, har sai an samu cikakkiyar nasara”. A cewar Buhari.

Sauran ‘yan tawagar tsaron sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali Baba, Darakta-Janar na Hukumar DSS, Yusuf Magaji Bichi, Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, Ambasada Ahmed Rufa’i Abubakar da shugaban tsaro Jami’in leken asiri, Manjo Janar Samuel Adebayo.

 

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp