fidelitybank

Tsaro: Amurka da Rasha za su gana a kan Ukraine

Date:

Jami’an Amurka da na Rasha za su yi shawarwari kan harkokin tsaro a ranar 10 ga watan Janairu domin tattauna damuwarsu game da ayyukan sojan da su ke yi da kuma tunkarar tashin hankalin da a ke yi kan kasar Ukraine.

Mai magana da yawun gwamnatin Biden ne ya sanar da ranar da yammacin jiya Litinin, kuma ya ce akwai yiwuwar Rasha da NATO suma za su yi tattaunawa a ranar 12 ga watan Janairu, inda za a yi wani babban taro da suka hada da Moscow, Washington da sauran kasashen Turai a ranar 13 ga watan Janairu.

Mataimakin ministan harkokin wajen Rasha Sergei Ryabkov ya tabbatar da wadannan ranakun a jiya Talata, ya kuma ce yana fatan tattaunawar da Amurka za ta yi a Geneva za ta kaddamar da wani tsari da zai bai wa Moscow wani sabon garantin tsaro daga kasashen yammacin duniya.

Wannana matakin dai wani dogon buri ne na Moscow, wanda ya firgita kasashen Yamma ta hanyar tara dubunnan dakaru kusa da Ukraine cikin watanni biyun da suka gabata.

Ryabkov ya ce, za a gudanar da taron kungiyar tsaro ta NATO a ranar 12 ga watan Janairu a Brussels na kasar Belgium, yayin da tattaunawar ta ranar 13 ga wata za ta kunshi kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai mai shelwata a Vienna, wadda ta hada da Amurka da kawayenta na NATO, da kuma Rasha da Ukraine da sauran tsoffin jihohin Soviet.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

MuÆ™arraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon É—an majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp