Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya ce, tsansar talauci da koma bayan tattalin arziki su ne manyan abubuwan da ke haifar da masaloli tsaro a yankin arewacin Najeriya, inda ya yi gargaɗin cewa muddin ba a magance su gaba ɗaya ba to yankin zai ci gaba da fuskantar matsalolin tashe-tashen hankaln.
Gwamnan ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Sunday Politics na gidan talibijin na Channels, inda ya ce gwamnatinsa ta soma ne da fito da hanyoyin yaƙi da talauci da rashin aikin yi tsakanin matasa, inda ya alaƙanta hakan ga irin ƙwarewar da ya ya samu lokacin da ya ke shugaban kwamitin da ke lura da bankuna na majalisar dattawan a lokacin yana ɗan majalsar dattawan.
“Lokacin da aka zaɓe ni a matsayin gwamnan Kaduna, abinda na soma yi shi ne duba girman matsalar talaucin da ake fama da ita, ba wai a jihata kaɗai ba a’a duka yankin arewa. Na taɓa riƙe muƙamin shugaban kwamitin da ke lura da harkokin bankuna na majalisar dattawa. Ina da bayanai da dukan alƙalumman da aka tattara daga Sashen Bunƙasa Babban Bankin Najeriya (CBN). Ina mai tabbatar maka cewa girman talaucin da ake da shi a shekarar 2023, lokacin da muka zo ya kai wani matsayi mai muni” in ji gwamnan.
A cewar sa fiye da kashi 60 zuwa 65 cikin ɗari na mutanen arewacin Najeriya – musamman a shiyar arewa maso yamma – na fama da tsananin talauci a lokacin da ya zama gwamman jihar Kaduna.
Uba Sani ya ce hakan na iya sa matasa da dama su shiga aikin ta’addanci kasancewar ƴanbindiga za su iya ɗaukar su haya domin kai hare-hare.