fidelitybank

Tsantsar talauci ne ke jawo rashin tsaro a Arewa – Uba Sani

Date:

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya ce, tsansar talauci da koma bayan tattalin arziki su ne manyan abubuwan da ke haifar da masaloli tsaro a yankin arewacin Najeriya, inda ya yi gargaɗin cewa muddin ba a magance su gaba ɗaya ba to yankin zai ci gaba da fuskantar matsalolin tashe-tashen hankaln.

Gwamnan ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Sunday Politics na gidan talibijin na Channels, inda ya ce gwamnatinsa ta soma ne da fito da hanyoyin yaƙi da talauci da rashin aikin yi tsakanin matasa, inda ya alaƙanta hakan ga irin ƙwarewar da ya ya samu lokacin da ya ke shugaban kwamitin da ke lura da bankuna na majalisar dattawan a lokacin yana ɗan majalsar dattawan.

“Lokacin da aka zaɓe ni a matsayin gwamnan Kaduna, abinda na soma yi shi ne duba girman matsalar talaucin da ake fama da ita, ba wai a jihata kaɗai ba a’a duka yankin arewa. Na taɓa riƙe muƙamin shugaban kwamitin da ke lura da harkokin bankuna na majalisar dattawa. Ina da bayanai da dukan alƙalumman da aka tattara daga Sashen Bunƙasa Babban Bankin Najeriya (CBN). Ina mai tabbatar maka cewa girman talaucin da ake da shi a shekarar 2023, lokacin da muka zo ya kai wani matsayi mai muni” in ji gwamnan.

A cewar sa fiye da kashi 60 zuwa 65 cikin ɗari na mutanen arewacin Najeriya – musamman a shiyar arewa maso yamma – na fama da tsananin talauci a lokacin da ya zama gwamman jihar Kaduna.

Uba Sani ya ce hakan na iya sa matasa da dama su shiga aikin ta’addanci kasancewar ƴanbindiga za su iya ɗaukar su haya domin kai hare-hare.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp