Gwamna jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yi murnar nasarar da tsaginsa ya samu a kotun daukaka kara.
A ranar Alhamis ne kotun a Abuja ta baiwa Ganduje nasara wanda ya ce, tsagin G7 tun asali kan karya suka shuka kararsa, saboda haka babu yadda za ayi su samu nasara.
Tsagin Shekarau sun lashi takobin daukaka kara kotun koli, sakamakon tika su da kasa.
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi jawabinsa na farko, bayan nasarar da tsaginsa ta samu.
Cikin tsakkiyar manyan jami’an gwamnati da kwamishinan sa, Musa Iliyasu Kwankwaso, gidan hutun jihar Kano dake unguwar Asokoro Abuja, Ganduje ya bayyana godiyara bisa al’ummar Kano.