fidelitybank

Tsadar rayuwa ta ƙaru da kashi 19 cikin ɗari a wata ɗaya a Najeriya – NBS

Date:

Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce tsadar rayuwa a ƙasar ta ƙaru da kashi 19.2 cikin ɗari a watan Yuni na wannan shekara 2024, kaɗai, wanda hakan ya zarta ƙarin da aka samu a watan Mayu da ya gabata na naira 1,041.

Wannan yana ƙunshe ne a cikin sabon rahoton da hukumar ta fitar, na yawan kuɗin da yawancin mutane aƙalla za su kashe wajen sayen abinci mai gina jiki a rana, inda ƙaruwar ta kasance da naira 1,241 a watan na Yuni.

A watan na Yuni hauhawar farashin kaya da ayyuka ta ƙaru zuwa kashi 34.19 cikin ɗari, inda ta ƙaru da kashi 0.24 cikin ɗari idan aka kwatanta da hauhawar a watan Mayun 2024, kamar yadda hukumar ta nuna.

Wannan mizani da ake amfani da shi wajen kiyasin matsayin rayuwar jama’a a duniya, bai ƙunshi kuɗin sufuri da kuɗin haɗa abincin ba.

A cikin watan na Yuni tsadar rayuwar ta fi girma a yankin kudu maso yamma, inda take naira 1,545 a kan duk magidanci ɗaya a rana, yayin da a yankin arewa maso yamma take naira 956.

A matakin jihohi, Ekiti, ita ce ta fi ganin karuwar tsadar da naira 1,640, sai Ogun mai naira 1,599, sai kuma Osun mai naira 1,557.

Jihar da tsadar take kafi kankanta ita ce Katsina mai naira 878, sai Kano mai naira 926 sai kuma Jigawa mai naira 937

Idan kuwa ana maganar sashe ne to sashen kudu maso yamma ya fi ganin tashin tsadar rayuwar inda aka samu 1,545 a rana sai kuma yankin kudu maso kudu mai naira1,376.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp