Kamfanonin jiragen sama na Najeriya sun ce sun dakatar da ayyukansu saboda karancin man fetur.
A ranar Laraba, Air Peace, Dana Air, Ibom Air, Aero Contractors, da sauran kamfanonin jiragen sama sun ba da sanarwar kawo cikas a jadawalin zirga-zirgar jiragen sama, sakamakon matsalar man fetur da ta addabi al’ummar kasar.
“Abin takaici, karancin man fetur ya fara yin tasiri sosai a ayyukanmu saboda da alama za mu fuskanci matsalar tashin jirage a yau da kuma kwanaki masu zuwa har sai lamarin ya lafa,” in ji sanarwar da Air Peace.
“Rikicin man fetur na jiragen sama na daukar sabon salo kuma ya ci gaba da shafar ayyukanmu.”
Ibom Air ya yi bayanin cewa,“Ayyukansa sun gamu da wani yanayi a yau inda ba a samun karancin man jiragen sama, sabili da haka babu shi a kusan dukkan wuraren da jirgin ya nufa.”
“Ba mu da wata alamar lokacin da za a warware matsalar. Duk da haka, muna aiki tare da takwarorinmu na kamfanonin jiragen sama da masu samar da mai don samun mafita,” sanarwar ta Ibom Air ta bayyana. A cewar rahoton OSG.