Kungiyar kwararrun masu yin burodi ta kasa, ta yi barazanar rufe gidajen burodi, sakamakon karin farashin man dizal a ‘yan kwanakin da suka gabata.
A wani taron manema labarai jiya a Owerri, babban birnin jihar, shugaban kungiyar na jihar, Cif Osmond Nkeoma, ya ce, idan ba a yi wani abu na shawo kan hauhawar farashin biredi ba, to ba za a sake samun sauki ga talaka ba.
Ya kara da cewa farashin man Dizal, man kayan lambu da sukari ya wuce gona da iri da masu yin burodin za su iya samu. “Muna matukar damuwa game da karuwar farashin dizal, man kayan lambu da sukari, wadanda ke da mahimmanci wajen samar da burodi.
“A na sayar da Diesel akan Naira 600 zuwa sama da kowace lita, sukari an barwa Dangote ne kawai ya ke nomawa, ba ma ganin wasu kamfanoni kamar BUA, yanzu buhun sukari da muke saye kan Naira 20,500 yanzu ana sayar da shi kan Naira 25,000. , Man kayan lambu da muke sayan N26,000 yanzu ana sayar da shi kan N35,000,” Nkeoma ta koka.