fidelitybank

Trump zai koro ‘yan Najeriya sama da 200

Date:

Hukumomi a Amurka sun rattaba sunayen ‘yan Najeriya 201 da za su kora zuwa gida yayin da Shugaba Donald Trump ke ci gaba da aiwatar da shirin korar baƙin haure daga ƙasar.

Daga cikin waɗanda aka tsara mayarwa gidan har da fursunoni, da waɗanda suka aikata laifuka, kamar yadda Ƙaramar Ministar Harkokin Waje ta Najeriya Bianca Odumegwu-Ojukwu ta bayyana a shafinta na X.

Ta ce ta bayyana wa jakadan Amurka Richard Mills Jr damuwar gwamnatin Najeriya game da mutanen lokacin da ya kai mata ziyara a Abuja.

“Zuwa yanzu, an faɗa mana cewa akwai ‘yan Najeriya kusan 201 a sansanonin jami’an shige da fice na Amurka, kuma an tantance 85 da za a dawo da su,” in ji ta.

“Wannan ba mazauna Amurka kawai ya shafa ba, har da ‘yan’uwansu a Najeriya da suka dogara da su, da yaran da suke biya wa kuɗin makaranta.

“A matsayinmu na ƙasa, muna so mu ji ko za a ba su isasshen lokaci wajen tattaro dukiyoyinsu. Ko kuma kawai zuba su za a yi a jirgi a dawo da su? Abin zai zama mai ɗimautarwa sosai musamman ga waɗanda ba su aikata wani laifi ba.”

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp