Hukumomi a Amurka sun rattaba sunayen ‘yan Najeriya 201 da za su kora zuwa gida yayin da Shugaba Donald Trump ke ci gaba da aiwatar da shirin korar baƙin haure daga ƙasar.
Daga cikin waɗanda aka tsara mayarwa gidan har da fursunoni, da waɗanda suka aikata laifuka, kamar yadda Ƙaramar Ministar Harkokin Waje ta Najeriya Bianca Odumegwu-Ojukwu ta bayyana a shafinta na X.
Ta ce ta bayyana wa jakadan Amurka Richard Mills Jr damuwar gwamnatin Najeriya game da mutanen lokacin da ya kai mata ziyara a Abuja.
“Zuwa yanzu, an faɗa mana cewa akwai ‘yan Najeriya kusan 201 a sansanonin jami’an shige da fice na Amurka, kuma an tantance 85 da za a dawo da su,” in ji ta.
“Wannan ba mazauna Amurka kawai ya shafa ba, har da ‘yan’uwansu a Najeriya da suka dogara da su, da yaran da suke biya wa kuɗin makaranta.
“A matsayinmu na ƙasa, muna so mu ji ko za a ba su isasshen lokaci wajen tattaro dukiyoyinsu. Ko kuma kawai zuba su za a yi a jirgi a dawo da su? Abin zai zama mai ɗimautarwa sosai musamman ga waɗanda ba su aikata wani laifi ba.”