fidelitybank

Trump zai kori Jami’an FBI da suka kutsa gidansa bincike

Date:

Jami’an hukumar binciken manyan laifuka ta Amurka,FBI, wadanda suka gudanar da bincike a kan tuhumar da aka yi wa Shugaba Donald Trump,tuhumar da aka yi watsi da ita yanzu suna fuskantar kora daga aiki a wani mataki na yin garambawul a hukumar.

Kafofin yada labaran Amurka sun ruwaito cewa gomman jami’an hukumar ta FBI da suke da hannu a binciken magoya bayan Trump ma da suka yi tarzoma da kutse a ginin majalisar dokoki kasar, Capitol, ranar 6 ga watan Janairun 2021 su ma suna fuskantar raba su da aiki.

Jaridar Washington Post ta ce ko a ranar Litinin an kori wasu jami’an ma’aikatar shari’a ta Amurka da suka yi aikin shari’ar magoya bayan Trump kan tarzomar ginin majalisar.

Jaridar ta ruwaito cewa an kori jami’an ne saboda mai rikon mumakin babban lauyan gwamnati, James McHenry, na ganin ba za su da ce da aiwatar da manufofin Trump ba.

Ita ma kafar CNN ta ruwaito cewa akalla manyan jami’an FBI shida aka bai wa umarnin ko dai su yi ritaya ko su sauka daga aiki ko kuma a kore su zuwa jibi Litinin.

Sanata Dick Durbin, babban dan majalisar dattawa na jam’iyyar Democrat, wanda ke kwamitin kula da harkokin shari’a, ya yi kakkausar suka a kan korar.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp