fidelitybank

Trump zai kori Jami’an FBI da suka kutsa gidansa bincike

Date:

Jami’an hukumar binciken manyan laifuka ta Amurka,FBI, wadanda suka gudanar da bincike a kan tuhumar da aka yi wa Shugaba Donald Trump,tuhumar da aka yi watsi da ita yanzu suna fuskantar kora daga aiki a wani mataki na yin garambawul a hukumar.

Kafofin yada labaran Amurka sun ruwaito cewa gomman jami’an hukumar ta FBI da suke da hannu a binciken magoya bayan Trump ma da suka yi tarzoma da kutse a ginin majalisar dokoki kasar, Capitol, ranar 6 ga watan Janairun 2021 su ma suna fuskantar raba su da aiki.

Jaridar Washington Post ta ce ko a ranar Litinin an kori wasu jami’an ma’aikatar shari’a ta Amurka da suka yi aikin shari’ar magoya bayan Trump kan tarzomar ginin majalisar.

Jaridar ta ruwaito cewa an kori jami’an ne saboda mai rikon mumakin babban lauyan gwamnati, James McHenry, na ganin ba za su da ce da aiwatar da manufofin Trump ba.

Ita ma kafar CNN ta ruwaito cewa akalla manyan jami’an FBI shida aka bai wa umarnin ko dai su yi ritaya ko su sauka daga aiki ko kuma a kore su zuwa jibi Litinin.

Sanata Dick Durbin, babban dan majalisar dattawa na jam’iyyar Democrat, wanda ke kwamitin kula da harkokin shari’a, ya yi kakkausar suka a kan korar.

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp