fidelitybank

Trump zai kakaba sabon haraji ga kasashen duniya

Date:

Shugaban Amurka Donald Trump zai sanar da sabbin harajin a yayin wani jawabin da zai yi a lambun Rose da ke fadar White House a ranar Laraba.

Hakan na zuwa ne a yayin da kallo ya koma Amurkan, inda duniya ke sauraron abin da sanarwar za ta ƙunsa, ganin tawagar da ke aiki da shugaban ƙasar sun yi gum a kan bayanai game da sabbin harajin.

A watan Maris ɗin da ya wuce, Mista Trump ya ce sabbin harajin za su zama tamkar rama wa kura aniyarta ne, don haka Amurka za ta sanya harajin daidai da yadda ƙasashe suka sanya mata.

Yayin da daga bisani kuma ya nuna cewa harajin zai iya zama ƙasa da abin da ƙasashe ke cajin Amurka.

Sai dai babu tabbacin taƙamaimai waɗanda harajin zai shafa, ko zai zama bai ɗaya ga kowa.

Sai dai akwai sabon haraji na kashi 25 cikin ɗari, a kan motoci da za a shigar Amurka wanda zai fara aiki a ranar Laraba.

Yayin da kayan motoci suma za su fuskanci irin wannan harajin a cikin watanni masu zuwa.

Tuni Amurkar ta fara aiwatar da wasu sabbin harajin a cikin watan Maris, kamar wanda ya shafi ƙarafa da goronruwa ko sanholo da ake shigarwa ƙasar.

Inda ƙasar ta ɗaga harajin zuwa kashi 25 cikin ɗari. Kuma tuni ta ƙara haraji kan duka kayayyakin da China ke shigarwa Amurkar, zuwa kashi 20 cikin ɗari.

Ƙasar Canada ta rama abin da Amurka ta yi mata, inda ta sanya harajin kashi 25 cikin ɗari kan ƙarafa da sanholo.

Yayin da China ta rama, inda ta kai harajin shigar mata da wasu kayan gona daga Amurka ke yi, zuwa kashi 10- 15 cikin ɗari.

Tarayyar Turai ta yi gargaɗin ɗaukar matakan ramuwa, yayin da Burtaniya ta ce tana jiran duk abin da Amurkan za ta yi.

Amma ranar wanka ba a ɓoyon cibi, domin a yau Amurkar za ta sanar da sabbin harajin da za ta sanya wa abokan hulɗarta na kasuwanci.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp