Tsohon shugaban Amurka, Donal Trump, ya ce, zai daukaka kara bayan samunsa da laifi da kotun New York ta yi ranar Alhamis.
Cikin wani jawabi na tsawon miti 40 da ya gabatar wa manema labarai, mista Trump ya ce, Za su daukaka kara kan wannan balahirar’.
Trump ya yi korafi kan matakin alkalin kotun da ya same shi da laifi.
Tsohon shugaban ya kuma zargi alkalin da rashin bai wa bangarensa damar kare kansu a shari’ar
Ya kuma ce, alkalin ya hana su gabatar da shaidu, sannan ya kuma hana su yi magana a kotun, inda ya yi alawadai da alkalin kotun bisa umarnin da ya yanke a kansa.
Tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya zama shugaban Amurka na farko da za a yankewa hukunci a kan tuhuma, bayan da masu taimaka wa alkali yanke hukunci suka same shi da laifi a tuhume-tuhume 34 da ake yi masa.
Dukkan tuhume-tuhumen na da alaka da karyar da ya yi a harkokin kasuwancinsa domin boye kudin da ya bayar na toshiyar baki a kan alakarsu da mai fitowa a fina-finai Stormy Daniels a lokacin gangamin yakin neman zaben shugaban kasar a 2016.