fidelitybank

Trump ya yi barazanar daina bai wa Afirka ta Kudu tallafi

Date:

Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce, zai katse duk wani tallafi da ƙasarsa ke bai wa Afirka ta kudu bisa zargin ta da kwace filaye da kuma nuna wariya ga wani ɓangare na al’umma.

A watan da ya gabata ne Shugaba Cyril Ramaphosa ya sanya hannu kan wani ƙudirin doka da ya ba da damar kwace filaye ba tare da biyan diyya ba a wasu lokuta.

A shafinsa na Truth, Trump ya ce ”zan katse duk wani tallafi ga Afirka ta kudu har sai an kammala gudanar da cikakken bincike kan lamarin.”

A cewar alƙaluman gwamnatin Amurka, ƙasar ta ware dala miliyan 440 domin tallafi ga Afirka ta kudu a shekarar 2023.

Sai dai wasu masu fashin baƙi na nuna fargaba kan mummunar sakamakon da dokar za ta iya samarwa kwatankwancin yadda aka samu a Zimbabwe wadda kwace filaye ya yi sanadin ruguza tattalin arziƙin kasar ya kuma kori masu zuba jari.

Batun mallakar filaye matsala ce da ta daɗe tana damun Afirka ta kudu ganin cewa fararen fata ne ke cigaba da mallakar akasarin gonaki a ƙasar, shekaru 30 bayan kawo ƙarshen mulkin wariyar launin fata. In ji BBC.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp