Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce, zai katse duk wani tallafi da ƙasarsa ke bai wa Afirka ta kudu bisa zargin ta da kwace filaye da kuma nuna wariya ga wani ɓangare na al’umma.
A watan da ya gabata ne Shugaba Cyril Ramaphosa ya sanya hannu kan wani ƙudirin doka da ya ba da damar kwace filaye ba tare da biyan diyya ba a wasu lokuta.
A shafinsa na Truth, Trump ya ce ”zan katse duk wani tallafi ga Afirka ta kudu har sai an kammala gudanar da cikakken bincike kan lamarin.”
A cewar alƙaluman gwamnatin Amurka, ƙasar ta ware dala miliyan 440 domin tallafi ga Afirka ta kudu a shekarar 2023.
Sai dai wasu masu fashin baƙi na nuna fargaba kan mummunar sakamakon da dokar za ta iya samarwa kwatankwancin yadda aka samu a Zimbabwe wadda kwace filaye ya yi sanadin ruguza tattalin arziƙin kasar ya kuma kori masu zuba jari.
Batun mallakar filaye matsala ce da ta daɗe tana damun Afirka ta kudu ganin cewa fararen fata ne ke cigaba da mallakar akasarin gonaki a ƙasar, shekaru 30 bayan kawo ƙarshen mulkin wariyar launin fata. In ji BBC.