fidelitybank

Trump ya tsallake rijiya da baya yayin da aka harbe shi

Date:

Hukumar Tsaron Amurka FBI ta tabbatar da cewa an yi yunkurin hallaka tsohon shugaban kasar Donald Trump.

Wani dan bindiga ne ya bude wuta a wurin yakin neman zaben tsohon shugaban kasar Donald Trump.

Ba a san dalilin maharin na son kashe tsohon shugaban ba, kana ba a sanar da sunansa ba har kawo yanzu.

Hotunan da aka yaÉ—a a Internet sun nuna lokacin da Donald Trump ya sunkuya cikin gaggawa ya buya a karkashin abun magana, yayin da yake tsaka da jawabi a kan duro.

Nan da nan jami’an tsaro na yan sanda da wadanda ke ba shi kariya suka kewaye shi suka yi masa rumfa, daga bisani suka fice da shi a gaggauce.

An fita da shi yana takawa dakyar, jini na zuba a kunnensa da fuskarsa.

Magoya bayansa sun rika yarda allunan goyon bayansa suna ranta a na kare, wasu na kwantawa a kasa don kare kansu.

Cikin yan mintuna kalilan wurin ya watse baki daya.

A cikin wata sanarwa da hukumar kare fararen hula ta kasar ta fitar, ta ce Trump na cikin koshin lafiya kuma an kare rayuwarsa.

Sanarwar ta kara da cewa yanzu haka ana gudanar da bincike mai zurfi kuma za a fitar da karin bayani idan an samu.

Shugaba Biden ya bayyana a gaban manema labarai a mahaifarsa ta Delaware, inda yi Allah wadai da harin, yana cewa zai yi magana da abokin hamayyar na sa, domin taya shi alhini. In ji BBC.

Tuni suma yan siyasa daga jam’iyyar tsohon shugaban kasar Trump ta Republican har ma da abokan hamayyarsa na Democrats suka fara yin tir da harin, suna kuma addu’ar samun sauki da nuna goyon baya ga tsohon shugaban.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp