fidelitybank

Trump ya samu nasara a zaɓen fitar da gwani duk da haramcin kotu

Date:

Donald Trump ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar Republican a New Hampshire yayin da yake neman tsayawa takarar shugabancin Amurka a jam’iyyar.

Sakamakon kusan rabin kuri’un da aka kirga ya ba shi fiye da kashi hamsin da biyar cikin dari, yayin da abokiyar hamayyarsa da ta rage, tsohuwar jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Nikki Haley, ta samu kusan kashi arba’in da uku cikin dari.

Kuma ta lashi takobin ci gaba da neman takarar.

Yanzu dai an kirga sama da rabin kur’un zaben fid da gwanin na jihar ta New Hampshire, inda daman kamar yadda aka yi hasashe wanda zai yi nasara, tsohon shugaban Amurkar, Donald Trump yake gaban abokiyar hamayyarsa, guda daya tilo tsohuwar jakadiyar Amurka a majalisar dinkin duniya, Nikki Haley da kusan maki 10.

Akwai dai wakilai ko delegets, 22 a jihar, inda kafar yada labarai ta CBS, da ke mu’amulla da BBC a Amurkar ta yi hasashen cewa Trump zai samu akalla 12 daga ciki, yayin da Haley za ta samu akalla tara idan ta yi kokari, hakan zai sa Trump ya samu jumulla 32 kenan Haley ta kasance da 17.

Wanda zai zama gwani a zaben dai dole ne ya kasance ya samu deleget 1,215.

Zuwa yanzu dai Mista Trump ya kama wannan hanya ba ji ba gani , kuma nasara ce ga tsohon shugaban na Amurka da za ta kara masa karfi na zama dan takarar jam’iyyar Republican a babban zaben kasar a watan Nuwamba.

Tuni daman ya gabatar da jawabin nasara har sau biyu a cikin kwana 8. Sai dai kalamansa ga taron magoya bayansa a New Hampshire a wannan karon bayan ganin ya kama hanyar nasara sun kasance daban da wadanda ya yi ranar Litinin a Iowa.

A baya ya nuna muhimmancin hadin kan jam’iyyarsu tare da yaba wa abokan takararsa to amma a wannan karon ya caccaki abokiyar hamayyar tasa ne, Nikki Haley da ta rage, wadda ta yi jawabi ga magoya bayanta jim kadan kafin Trump ya shiga fage ya gabatar da nasa jawabin, inda ya ce tana magana kamar ita ce ta ci zaben.

Ya ce “dole in gaya muku abin ban sha’awa ne, saboda na ce, kai wannan irin nasara, to amma sai kawai wani ya shigo fagen ya yi kwalliya da kyau, a lokacin ana kan bakwai, to amma yanzu na shigo an ce 14. Amma ita ta shigo a lokacin ana bakwai, to amma dole ne mu yi abin da ya dace ga jam’iyyarmu,

Ta dage da, tana jawabi, na ce kai, kamar ta yi nasara, ba ta ci ba, ta fadi.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp