Shugabannin ƙungiyar Hamas sun ce, tsoma bakin da Donald Turmp ke yi a baya-bayan nan game da Gaza na ƙara dagula batun yarjejeniyar tsagaitar da ke rawa da aka cimma tsakanin ɓangarorin biyu.
A jiya Litinin Trump ya yi barazanar watsi da yarjejeniyar matuƙar Hamas ta gaza sakin ɗaukacin ƴan Isra’ila da take garkuwa da su.
Ɗaya daga cikin masu magana da yawun Hamas, Sami Abu Zuhri ya ce hanya ɗaya tilo ta tabbatar da cewa dukkanin waɗanda ake garkuwa da su sun koma gida ita ce ta hanyar martaba yarjejeniyar da aka cimma a watan jiya sau-da-ƙafa.
A jiya Litinin, Hamas ta yi barazanar jinkirta sakin sauran ƴan Isra’ila da take riƙe da su bisa zargin Isra’ilar da rashin martaba ƙa’idojin yarjejeniyar yadda ya kamata.
Hujjojin da Hamas ta bayar sun haɗa da cewa Isra’ila na yin cikas ga shigar kayan agaji zuwa Gaza da kuma sakin Falasɗinawan da ke hannunta.
Isra’ila ta yi watsi da zargin, sannan tana ƙara yawan dakarunta a kusa da yankin.