fidelitybank

Trump ya na dagula mana lisafi – Hamas

Date:

Shugabannin ƙungiyar Hamas sun ce, tsoma bakin da Donald Turmp ke yi a baya-bayan nan game da Gaza na ƙara dagula batun yarjejeniyar tsagaitar da ke rawa da aka cimma tsakanin ɓangarorin biyu.

A jiya Litinin Trump ya yi barazanar watsi da yarjejeniyar matuƙar Hamas ta gaza sakin ɗaukacin ƴan Isra’ila da take garkuwa da su.

Ɗaya daga cikin masu magana da yawun Hamas, Sami Abu Zuhri ya ce hanya ɗaya tilo ta tabbatar da cewa dukkanin waɗanda ake garkuwa da su sun koma gida ita ce ta hanyar martaba yarjejeniyar da aka cimma a watan jiya sau-da-ƙafa.

A jiya Litinin, Hamas ta yi barazanar jinkirta sakin sauran ƴan Isra’ila da take riƙe da su bisa zargin Isra’ilar da rashin martaba ƙa’idojin yarjejeniyar yadda ya kamata.

Hujjojin da Hamas ta bayar sun haɗa da cewa Isra’ila na yin cikas ga shigar kayan agaji zuwa Gaza da kuma sakin Falasɗinawan da ke hannunta.

Isra’ila ta yi watsi da zargin, sannan tana ƙara yawan dakarunta a kusa da yankin.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp