Aƙalla mutanen Indiya kimanin 100 da ake zargin sun shiga Amurka ta ɓarauniyar hanya ne ake sa ran za su isa jihar Punjab a yau.
Wani jirgin saman sojojin Amurka da ke ɗauke da mutanen ya bar birnin Texas a daren ranar jiya Talata.
Jami’ai a birnin Amritsar sun bayyana cewa a shirye su ke na karɓar mutanen.
Donald Trump ya sanya aikin korar dubban baƙin haure da ke zama a Amurka ba bisa ƙa’ida ba cikin muhimman tsare tsarensa.
Ya ce Firaministan Indiya Narendra Modi ya tabbatar masa cewa ƙasarsa za ta yi ‘abin da ya dace’ wajen ƙarbar waɗanda za a dawo da su.