Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta yi kira ga Amurka da ta janye ƙudurinta da ficewa daga cikin harkokin hukumar.
Hukumar ta bayyana haka ne a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na X, inda ta ce tana taka rawa wajen inganta lafiya da tsaron al’umma, ciki har da Amurka.
“Ta hanyar gano musabbabin cututtuka da inganta asibitoci da ganowa tare da kiyaye aukuwa ko yaɗuwar cututtuka ciki har da annoba.”
Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka na cikin ƙasashen da suka assasa hukumar a shekarar 1948, kuma tun a lokacin take taimaka wa ayyukan ƙungiyar tare da sauran mambobin hukumar guda 193.
A sama da shekara 70 da hukumar ke aiki, WHO da Amurka sun ceci rayuka da dama da ba za a iya ƙididdigewa ba, sannan ta kare yaɗuwar cututtuka da dama a ƙasashen duniya ciki har da Amurka.
“Ta hanyar wannan haɗakar, muka yaƙi cutar smallpox, sannan muna gab da yaƙar polio. Wannan ya sa muke fata Amurka za ta sake tunani, tare da janye ƙudurinta na ficewa daga hukumar ta lafiya domin kula da lafiyar miliyoyin mutane a duniya.”