fidelitybank

Trump ya janye kudurinsa na janye hannun Amurka daga hukumar mu – WHO

Date:

Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta yi kira ga Amurka da ta janye ƙudurinta da ficewa daga cikin harkokin hukumar.

Hukumar ta bayyana haka ne a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na X, inda ta ce tana taka rawa wajen inganta lafiya da tsaron al’umma, ciki har da Amurka.

“Ta hanyar gano musabbabin cututtuka da inganta asibitoci da ganowa tare da kiyaye aukuwa ko yaɗuwar cututtuka ciki har da annoba.”

Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka na cikin ƙasashen da suka assasa hukumar a shekarar 1948, kuma tun a lokacin take taimaka wa ayyukan ƙungiyar tare da sauran mambobin hukumar guda 193.

A sama da shekara 70 da hukumar ke aiki, WHO da Amurka sun ceci rayuka da dama da ba za a iya ƙididdigewa ba, sannan ta kare yaɗuwar cututtuka da dama a ƙasashen duniya ciki har da Amurka.

“Ta hanyar wannan haɗakar, muka yaƙi cutar smallpox, sannan muna gab da yaƙar polio. Wannan ya sa muke fata Amurka za ta sake tunani, tare da janye ƙudurinta na ficewa daga hukumar ta lafiya domin kula da lafiyar miliyoyin mutane a duniya.”

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp