Gwamnatin shugaban Amurka, Donald Trump ta umarci ofisoshin jakadancinta da ke faɗin duniya su dakatar da bai wa ɗalibai da sauran mutane da ke neman bizar ziyara zuwa ƙasar.
Gwamnatin ta ba da umarnin ne yayin da take faɗaɗa shirin binciken bada bisa ta hanyar tantace abubuwan da mutum ke wallafawa a shafukan sada zumunta, musamma ɗalibai.
Wasu daliban kuma da tuni suke Amurka an kwace bizarsu saboda shiga gangamin nuna goyon-bayan Falasdinawa.
Wannan na daga cikin matakan da Trump ke ɗauka na hana manyan makarantun Amurka da suka yi fice wajen dogaro da kuɗaden makaranta da suke samu daga ɗaliban ketare.
Kafin wannan lokaci fadar gwamnatin Amurka White House ta ce gwamnatin Trump ta buƙaci dukkanin ma’aikatun Amurka su datse tallafin da suke bai wa jami’ar Havard da suke amfani da shi wajen bada tallafin karatu.