Shugaba Trump na Amurka ya ƙara ƙaimi wajen shirinsa na ƙwace iko da Gaza tare da fitar da Falasɗinawa daga Zirin duk da suka da shirin nasa ke sha daga al’ummar duniya.
Trump ya shaidawa manema labarai cewa yana son ya saya tare da mallakar Gaza domin tabbatar da cewa Hamas ba ta sake tasiri ba.
Ya kuma bayyana cewa zai kula da Falasɗinawa tare da tabbatar da cewa sun yi rayuwa cikin aminci da kwanciyar hankali.
Ya kuma ce yana son sauran ƙasashen Larabawa da su shiga cikin sake gina wani ɓangare na Gaza.