Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya ce idan har Hamas ba ta saki sauran Isra’ilawan da take garkuwa da su a Gaza ba zuwa tsakar ranar Asabar, Isra’ila za ta soke yarjejeniyar tsagaita wuta, sannan ayi duk bala’in da za’ayi.
Ya kuma ce zai iya dakatar da tallafin da suke ba ƙasashen Jordan da Masar idan har suka ƙi amincewa ya tsugunnar da Falasdinawa da yake son kwashewa daga Gaza.
Kalaman na sa na zuwa ne bayan sanarwar da Hamas ta yi na dakatar da sakin Isra’ilawan da ta yi garkuwa da su har sai abunda hali ya yi, inda ta zargi Isra’ila da karya dokokin tsagaita wuta.