fidelitybank

Trump mai laifi ne dole ne mu hukunta shi – Iran

Date:

Iran ta musanta alaka da yunkurin kashe tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump.

Ofishin Jakadancin Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya ce zargin yunkurin kashe Trump “ba shi da tushe balle makama.”

Wani matashi dan shekara 20 ya harbe Trump a yunkurinsa na kashe shi a lokacin yakin neman zabensa a Butler da ke jihar Pennsylvania a ranar Asabar.

Yayin da mai harbin ya kusa harbe Trump, ma’aikatar sirri ta kashe matashin mai shekaru 20 a wurin.

Bayan faruwar lamarin, an zargi Iran da yunkurin kashe Trump a matsayin martani ga kisan Janar Soleimani.

Sai dai Ofishin Jakadancin Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana Trump a matsayin mai laifi wanda za a hukunta shi ta hanyar doka.

Rundunar ta kuma ce dan bindigar mai suna Thomas Matthew Crooks, ba shi da wata alaka da kasar ta.

“A mahangar Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Trump ya kasance mai laifi wanda dole ne a gurfanar da shi tare da hukunta shi a gaban kotun shari’a saboda ba da umarnin kashe Janar Soleimani.

“Iran ta zabi hanyar doka don gurfanar da shi a gaban shari’a,” in ji shi.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp