fidelitybank

Toshon kakakin Ganduje, Salihu Tanko Yakasai ya fice daga APC

Date:

 

 

 

 

 

Tsohon Mai taimakawa Gwamnan Jihar Kano a kan harkokin yada labarai, Salihu Tanko Yakasai ya fice da ga jam’iyyar APC.

A yau Litinin ne dai Yakasai ya sanar da ficewar ta sa da ga jam’iyar a yayin taron manema labarai a Kano.

Ya ce ya ɗauki matakin barin jam’iya mai mulkin ne sabo da rashin cika alkawuran da ta yi wa al’ummar ƙasar nan.

Yakasai, wanda a ke yi wa lakabi da Dawisu, yace Jam’iyyar APC ta gaza sauke mafi yawa daga cikin nauye-nauyen data daukarwa ƴan Nijeriya, dama abubuwan da ya kamata a ce gwamnati ta yiwa al’ummar ta.

“Da ni a ka yi tallan jam’iyyar APC a dukkanin mafi yawa daga cikin jihohin Nijeriya , kuma mun yiwa al’ummar kasar nan alkawura. Amma ni da kaina na gamsu da cewa jam’iyyar ta gaza dauke alkawuran data yiwa yan kasa”. Inji Yakasai

Salihu Yakasai, wanda Gwamnatin Kano ta kora da ga mukaminsa saboda irin kalaman da yake yi na sukar gwamnatin tarayya, ya ce ya dade ya na fadawa gwamnatoci gaskiya tun lokaci da PDP ta ke kan mulki.

“Saboda irin matsalolin da ƴan ƙasar nan suke cikin na rashin tsaro, rashin baiwa yan kasa kyakykyawar rayuwa , sanya ƴan kasa cikin mawuyacin hali, da ma wasu matsalolin, shi ya sa na fice daga jam’iyyar APC a wannan rana”.inji Salihu Yakasai

Tanko Yakasai yace nan gaba kadan zai baiyana Inda zai koma domin cigaba da gwagwarmayar siyasa.

Sai dai kuma Salihu Yakasai ya yaba wa Gwamna Abdullahi Ganduje bisa bashi dama ya hidimta wa Jihar Kano, inda ya ce alakar shi da gwamnan ta zama ta uba da ɗa.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp