fidelitybank

Toshon kakakin Ganduje, Salihu Tanko Yakasai ya fice daga APC

Date:

 

 

 

 

 

Tsohon Mai taimakawa Gwamnan Jihar Kano a kan harkokin yada labarai, Salihu Tanko Yakasai ya fice da ga jam’iyyar APC.

A yau Litinin ne dai Yakasai ya sanar da ficewar ta sa da ga jam’iyar a yayin taron manema labarai a Kano.

Ya ce ya ɗauki matakin barin jam’iya mai mulkin ne sabo da rashin cika alkawuran da ta yi wa al’ummar ƙasar nan.

Yakasai, wanda a ke yi wa lakabi da Dawisu, yace Jam’iyyar APC ta gaza sauke mafi yawa daga cikin nauye-nauyen data daukarwa ƴan Nijeriya, dama abubuwan da ya kamata a ce gwamnati ta yiwa al’ummar ta.

“Da ni a ka yi tallan jam’iyyar APC a dukkanin mafi yawa daga cikin jihohin Nijeriya , kuma mun yiwa al’ummar kasar nan alkawura. Amma ni da kaina na gamsu da cewa jam’iyyar ta gaza dauke alkawuran data yiwa yan kasa”. Inji Yakasai

Salihu Yakasai, wanda Gwamnatin Kano ta kora da ga mukaminsa saboda irin kalaman da yake yi na sukar gwamnatin tarayya, ya ce ya dade ya na fadawa gwamnatoci gaskiya tun lokaci da PDP ta ke kan mulki.

“Saboda irin matsalolin da ƴan ƙasar nan suke cikin na rashin tsaro, rashin baiwa yan kasa kyakykyawar rayuwa , sanya ƴan kasa cikin mawuyacin hali, da ma wasu matsalolin, shi ya sa na fice daga jam’iyyar APC a wannan rana”.inji Salihu Yakasai

Tanko Yakasai yace nan gaba kadan zai baiyana Inda zai koma domin cigaba da gwagwarmayar siyasa.

Sai dai kuma Salihu Yakasai ya yaba wa Gwamna Abdullahi Ganduje bisa bashi dama ya hidimta wa Jihar Kano, inda ya ce alakar shi da gwamnan ta zama ta uba da ɗa.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...
X whatsapp