Shugaban hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta EFCC a Najeriya, Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar ta bankado wani gwamna mai ci na wata jihar Arewacin kasar da ya kwashi tsabar kudi har Naira biliyan 60 daga asusun jiharsa a cikin shekaru 6.
Hukumar ta bayyana haka ne a sakon da take aike wa manema labarai na wata-wata mai taken “EFCC Alert”
Abdulrasheed Bawa ya yi wannan ikarin ne game da batun a wata hirarsa da mujallar da hukumar ta ke wallafawa, ya ce gwamnan da a ka gano na wata jiha ce da ke Arewa ta tsakiya ko da ya ke bai fadi sunansa ba.
Ya kuma ce, “Zan iya gaya muku a kyauta cewa, sabon sashen da muka bude kan leken asiri ya na aiki tukuru, kuma ya na bankado abubuwa da dama. Daya daga cikin su shi ne wani gwamna a wata jiha ta Arewa ta tsakiya, mun gano cewa cikin shekara Shida da su ka gabata (mutum daya) ya cire tsabar kudin da suka kai Nair biyian 60”.
“Muna kallon abubuwan da ya ke yi, kuma ina tabbatar muku cewa bayan mun kammala bincike, za mu sanar da ‘yan Najeriya kan abubuwan da mu ka yi a bayan fage game da laifukan da a ke aikatawa ta amfani da shafukan intanet”. A cewar Bawa.
Ya kuma kara da cewar, “Ya kasance tare da mu kwana biyu kuma an sake shi; Ana ci gaba da gudanar da bincike, amma muna yin taka-tsantsan da taka tsantsan, domin haka ba za a tuhume mu da yin shari’ar kafafen yada labarai ba. Ina tabbatar muku cewa muna aiki a kansu, ba ma son yin magana game da al’amuran da a ke bincike, kuma tabbas mun gayyaci tsohon gwamna (Lucky Igbinedion), domin yi masa tambayoyi shi ma”. inji Bawa