fidelitybank

Tonon Asiri: Mun gano gwamnan Arewa da ya kwashe kudi Naira biliyan 60 – EFCC

Date:

Shugaban hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta EFCC a Najeriya, Abdulrasheed Bawa ya ce hukumar ta bankado wani gwamna mai ci na wata jihar Arewacin kasar da ya kwashi tsabar kudi har Naira biliyan 60 daga asusun jiharsa a cikin shekaru 6.

Hukumar ta bayyana haka ne a sakon da take aike wa manema labarai na wata-wata mai taken “EFCC Alert”

Abdulrasheed Bawa ya yi wannan ikarin ne game da batun a wata hirarsa da mujallar da hukumar ta ke wallafawa, ya ce gwamnan da a ka gano na wata jiha ce da ke Arewa ta tsakiya ko da ya ke bai fadi sunansa ba.

Ya kuma ce, “Zan iya gaya muku a kyauta cewa, sabon sashen da muka bude kan leken asiri ya na aiki tukuru, kuma ya na bankado abubuwa da dama. Daya daga cikin su shi ne wani gwamna a wata jiha ta Arewa ta tsakiya, mun gano cewa cikin shekara Shida da su ka gabata (mutum daya) ya cire tsabar kudin da suka kai Nair biyian 60”.

“Muna kallon abubuwan da ya ke yi, kuma ina tabbatar muku cewa bayan mun kammala bincike, za mu sanar da ‘yan Najeriya kan abubuwan da mu ka yi a bayan fage game da laifukan da a ke aikatawa ta amfani da shafukan intanet”. A cewar Bawa.

Ya kuma kara da cewar, “Ya kasance tare da mu kwana biyu kuma an sake shi; Ana ci gaba da gudanar da bincike, amma muna yin taka-tsantsan da taka tsantsan, domin haka ba za a tuhume mu da yin shari’ar kafafen yada labarai ba. Ina tabbatar muku cewa muna aiki a kansu, ba ma son yin magana game da al’amuran da a ke bincike, kuma tabbas mun gayyaci tsohon gwamna (Lucky Igbinedion), domin yi masa tambayoyi shi ma”. inji Bawa

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp