Ƙungiyar siyasar nan mai suna The National Movement (TNM), wacce tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya kafa kwanan nan, ta amince da shiga sabuwar jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP).
Da yake jawabi bayan wani taro na sa’o’i bakwai a Abuja, shugaban riko na TNM na kasa, John Chris Ifeimeje, ya ce, kungiyar ta yanke shawarar daukar jam’iyyar NNPP ne, domin ceto kasar nan daga mummunan shugabanci da jam’iyya mai mulki ta shirya.
An kuma nada Ifeimeje a matsayin shugaban kwamitin riko na jam’iyyar NNPP. Ya nada tsohon ministan matasa da wasanni, Solomon Dalung da Buba Galadima a matsayin wani bangare na kwamitin riko.
Mambobin sun hada da Dr Boniface Aniebonam a matsayin shugaban kwamitin amintattu (BoT); Sanata Suleiman Hunkuyi, mataimakin shugaba; Hon. Oladipo Olayoku, Sakataren kasa; Major Gilbert Agbo, Sakataren Yada Labarai na kasa; da Farfesa Rufa’i Ahmed Alkali, sakataren kungiyar na kasa; da sauransu.
A cewarsa, kungiyar tun bayan kaddamar da kungiyar a watan da ya gabata, ta samu gagarumin martani daga sassa daban-daban na kasar, kuma dimbin jama’a da kungiyoyi sun yi ta tururuwa zuwa sakatariyar TNM ta kasa, domin tantancewa da shiga kungiyar.
Ya kara da cewa jam’iyyar ta tsayar da ranar 30 ga watan Maris, domin gudanar da babban taronta na kasa.