fidelitybank

TNM ta amince da shiga sabuwar jam’iyyar NNPP

Date:

Ƙungiyar siyasar nan mai suna The National Movement (TNM), wacce tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya kafa kwanan nan, ta amince da shiga sabuwar jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP).

Da yake jawabi bayan wani taro na sa’o’i bakwai a Abuja, shugaban riko na TNM na kasa, John Chris Ifeimeje, ya ce, kungiyar ta yanke shawarar daukar jam’iyyar NNPP ne, domin ceto kasar nan daga mummunan shugabanci da jam’iyya mai mulki ta shirya.

An kuma nada Ifeimeje a matsayin shugaban kwamitin riko na jam’iyyar NNPP. Ya nada tsohon ministan matasa da wasanni, Solomon Dalung da Buba Galadima a matsayin wani bangare na kwamitin riko.

Mambobin sun hada da Dr Boniface Aniebonam a matsayin shugaban kwamitin amintattu (BoT); Sanata Suleiman Hunkuyi, mataimakin shugaba; Hon. Oladipo Olayoku, Sakataren kasa; Major Gilbert Agbo, Sakataren Yada Labarai na kasa; da Farfesa Rufa’i Ahmed Alkali, sakataren kungiyar na kasa; da sauransu.

A cewarsa, kungiyar tun bayan kaddamar da kungiyar a watan da ya gabata, ta samu gagarumin martani daga sassa daban-daban na kasar, kuma dimbin jama’a da kungiyoyi sun yi ta tururuwa zuwa sakatariyar TNM ta kasa, domin tantancewa da shiga kungiyar.

Ya kara da cewa jam’iyyar ta tsayar da ranar 30 ga watan Maris, domin gudanar da babban taronta na kasa.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp