Wata Amarya mai ƙarfin hali ta cakawa uwar gidan ta wuka har ta yi sanadiyar mutuwar ta, saboda saɓanin kwanciyar aure da suka samu da Maigidan ta.
Lamarin ya faru ne a jihar Ondo, kuma matar ta ce, ba ta yi nufin kashe uwar gidan ta ba, fushi ne kan abin da mijin ya yi mata.
Ta ce ta jiyo uwar gida da maigida suna zaginta yayin da suke kwanciyar aure a ɗaki, kuma mijin ya barta kwance ta na jiran shi.
Rebecca Nicodemus, yar kimanin shekara 25 a duniya ta daba wa Uwar Gida wuka har lahira jim kaɗan, bayan kammala kwanciyar aure da Maigidansu.
A cewar, The Nation, ta ce Amarya Rebecca ta shiga matsancin kishi, saboda mijinta ya taso ya barta a kan gado suna tsaka da saduwar aure, domin ya koma wurin uwar gidan mai suna Precious.
Tuni ‘yan sanda suka yi ram da Amarya Rebecca kuma aka gurfanar da ita gaban Kotun Majirtire dake Akure kan tuhumar kisan kai.
Assalamu alaikum