fidelitybank

Tirkashi an yi garkuwa da sabon Baturen ‘Yan Sanda

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun yi garkuwa da wani jami’in ‘yan sanda reshen shiyya da aka mayar da shi sashin Pankshin na jihar Filato.

An yi garkuwa da sabon Baturen ‘Yan Sandan wato DPO din, wanda ba a iya tantance sunansa a ranar Laraba a otal din da ya sauka a karamar hukumar.

Wata majiya ta shaidawa DAILY POST cewa ‘yan bindigar da yawan gaske, sun mamaye otal din ne da misalin karfe 10:45 na dare, inda suka yi awon gaba da shi da bindiga, suka kuma kai shi inda ba a sani ba.

Ya kara da cewa, “masu garkuwa da mutane sun yi ta harbe-harbe da dama a iska kafin daga bisani su shiga otal din da misalin karfe 10:45 na dare. Ya kasance kamar DPO ne aka yi musu hari; sun harbe shi a kafa kafin a tafi da shi.”

A cewar majiyar, jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Filato da sauran jami’an tsaro na cikin dajin da ke yankin suna yin iyakacin kokarinsu na ganin sun kubutar da dan sandan daga hannun wadanda suka sace shi.

DSP Alfred Alabo, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, bai iya tabbatar da sace shi ba, saboda ba a amsa kiran da aka yi a wayarsa.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp