fidelitybank

Tirkashi an sace jariri a asibitin Bauchi

Date:

Hankula sun tashi a sashen masu haihuwa na Asibitin Koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi, bayan da aka sace wani jariri.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa uban jaririn ya ce ƴan biyu matarsa ta haifa a ranar Laraba, sai wata mata ta yi shiga irin ta malaman asibiti ta ce wa matarsa ɗaya daga cikin jariran ba shi da lafiya za a duba shi a wani sashen na asibitin.

Daga nan ta ɗauki yaron ta tafi ba ta sake komawa ba.

Uban jaririn Ibrahim Dallami Khalid ya ce, ya yi tsammanin matarsa ta san matar ne shi ya sa bai yi wata hoɓɓasa ba a lokacin da ya ganta.

“Daga baya bayan na bar asibitin sai matata ta cewa mahaifiyarta ta kawo mata ƙwai. Bayan ta tafi kawo ƙwan ne sai matar ta sake komawa ɗakin ta tambayi surukata ina za ta. Sai ta amsa mata ta wuce.

“Ita kuma matar sai ta yi amfani da damar ta zauna kusa da matata, ta ce mata ɗaya daga cikin jariran ba shi da lafiya za ta kai mata shi sashen da ake duba yara. Sai matata ta ƙyale ta ta ɗauke shi. Tun daga sannan ba a sake jin ɗuriyarta ba.”

Jaridar Daily Trust ta ce ta so jin ta bakin mai jegon amma ba ta cikin hayyacinta tun bayan faruwar lamarin.

Shugaban kwamitin ba da shawara na asibitin Dr. Haruna Liman ya bayyana lamarin a matsayin marar daɗi, kuma rundunar ƴan sandan jihar ta ce tuni ta ƙaddamar da bincike don kama wacce ake zargin.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...
X whatsapp