Shugaban Alkalan jihar Zamfara, Mai Shari’a Kulu Aliyu, ta kafa kwamitin mutum bakwai, domin gudanar da bincike kan tuhume-tuhumen da majalisar dokokin jihar ke wa mataimakin gwamnan Zamfara, Mahdi Gusau.
Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa, mai Shari’a Kulu Aliyu ta rantsar da kwamitin ne ranar Litinin, kuma ta nada tsohon Alkali, Tanko Soba, matsayin shugaban kwamitin.
Ayyukan kwamitin a cewarta, sun hada da bincike kan tuhumar almundahana, ci da ofis, saba kundin tsarin mulki da kuma yin abubuwan da basu dace ba.
A cewarta, kundin tsarin mulki ya daura mata nauyi a matsayin Alkalin Alkalan jihar ta nada kwamitin.
Ta kuma yi kira ga mambobin kwamitin suyi aiki tare kan zargin da akewa mataimakin gwamnan.