Wata mata ta rasa ranta, bayan da tirela ta ƙwace sannan ta afka a kanta a mahaɗar Mobil a karamar hukumar Suleja da ke jihar Neja.
Kwamandan hukumar kiyaye haɗura ta jihar, Kumar Tsukwam ya faɗa wa Daily Trust cewa lamarin ya faru ne lokacin da tirelar ta fito daga garin Diko zuwa Zuba, inda ta murkushe matar.
Ya ce mutane ukun ciki har da karamar yarinya sun samu munanan raunuka, kuma an garzaya da su zuwa babbar asibitin Suleja domin yi musu magani.
Kwamandan ya ce haɗarin ya afku ne tsakanin tireloli guda biyu sakamakon gudu fiye da kima da direban motar yake yi.
Ya kuma shawarci hukumomi da su gina gadar sama a mahaɗar ta Mobil da ya dangana da tsaunin Zuma da kuma Zuba.